Ta’addancin Isra’ila a Gaza:
An Sami Asarar Rayukan Sama da Mutane 61,330 da Mutane 152,359 da suka Sami Runuka tun Daga 7 ga Oktoba, 2023 Zuwa Yau Sakamakon Hare-haren Isra’ila a Gaza
Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta fitar da rahoton mutuwar mutane 72 da kuma mutane 314 da suka samu munanan raunuka a cikin sa’o’i 24 da suka gabata.
Mutane da dama ne masu fama da yunwa a Gaza suka haura kan wata rumfar wani shago bayan da wani akwati dauke da kayan agaji da ya fada a kai nauyin mutane sai suka yiwa rumfar yawa, sakamakon haka sai ta ruguzo kasa inda ta raunata mutane da dama.
Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta fitar rahotan adadin wadanda suka mutu sakamakon hare-haren Isra’ila tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023 ya kai mutane 61,330 da kuma mutanen da suka sami runuka sun kai mutane 152,359.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




