By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara
News

Ƴanbindiga sun cinna wa gonaki wuta a jihar Zamfara

Attajdid
Last updated: 2024/11/19 at 6:26 AM
Attajdid Published November 19, 2024
Share
SHARE

Wasu da ake zargin ƴanbindiga ne sun cinna wa gonakin manoma da dama wuta tare da yin garkuwa da mutane da dama a wasu ƙauyukan jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya

 

Maharan sun fara kai harin ne a garin Farin Ruwa da ke ƙaramar hukumar Maru da ke a jihar ta Zamfara, inda suka kone gonakin manoma.

 

Sun kuma kai irin wannan harin a ƙayukan Wanke da kuma Zargada inda suka ƙone amfanin gona.

 

Mazauna yankunan da ke iyaka da jihar Kebbi, sun ce ƴanbindigar sun sa sun tafka gagarumar hasarar amfanin gonar da suka noma da ya hada da masara da auduga, da wake da sauran su.

 

Maharan sun zo ne gungu-gungu tare da cinna wa gonakin masara da wake da dawa wuta, abin da kuma ya haifar da hasara mai ɗimbin yawa.

 

Sun kuma yi awon gaba da dimbin mutane inda suka ƙona gonaki da dama, kamar yadda wasu daga cikin manoman da suka tafka asarar suka shaida wa BBC.

 

“Muna cikin ƙunci da wahala, kodayaushe idan ba a kai farmaki ba to za a kashe, akwai matsala.”

 

Rahotani na cewa garuruwan Wanke da Zargada da Dan Godabe na daga cikin wadanda maharan suka addaba.

 

Wani da ya nemi a sakaya sunansa saboda dalilan tsaro, ya ce matakin da ‘yan bindigar suka dauka na kone gonaki da garkuwa da mutane domin neman kudin fansa, ya sa suna ganin kansu tamkar ba ƴan Najeriya ba.

 

Ya kuma yi zargin an kyale maharan na cin karensu babu babbaka, kuma babu abin da za su yi face zura ido ga kangin bautar da maharan suka saka su.

 

“Mutum ma bai sani ba sai ya je gonarsa ya iske ta bushe, sai mutum ya iske bala’in da ya iske sai dai kawai ya yi Kalmar Shahada,”

 

Sun kuma yi garkuwa da mutum bakwai bayan sun ƙona mana gonaki,” in ji wani mazauni yankin.

Mai Rahoto

Mujahid Muhammad Tasiu.

 

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid November 19, 2024 November 19, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Yanbindiga sun sace mutum 117 da hallaka wasu tara a Jihar Kebbi

Attajdid Attajdid May 29, 2025
Nijeriya ta Sayar da  Wutar Lantarkin Naira Biliyan 181.6 a Cikin Wata Tara
EndBadGovernance# Jigawa first Lady Advocates Inculcating Moral Discipline To Children#
Biyan kudaden jarabawar NBAIS – NAPAIS ta yaba wa Gwamnatin Jihar Kano
An Jikkita Sojojin Isra’ila 23 a Gaza da Lebanon 
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?