By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Hisbah Aikin Allah: Gwamna Amadu, Gwamnan Addini.
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > Uncategorized > Hisbah Aikin Allah: Gwamna Amadu, Gwamnan Addini.
Uncategorized

Hisbah Aikin Allah: Gwamna Amadu, Gwamnan Addini.

Attajdid
Last updated: 2025/05/21 at 7:07 AM
Attajdid Published May 21, 2025
Share
SHARE

Gwamnan addini, His Excellency Dr. Ahmad Aliyu Sokoto FCNA ya dawo da aikin Hisbah a Jihar Sokoto, bayan da tsohuwar gwamnatin baya ta soke aikin.

Kasancewar Sokoto cibiya ce ta addinin Musulunci kuma cibiya ce ta Daular Usmaniyya, tun bayan gwamnati baba Alu, Jihar Sokoto ba ta sake samun gwamna mai addini ba kamar wannan lokaci na Amadun Alu. Gwamnan ya dawo da aikin Hisbah ne bisa jagorancin Malam Usman Abdullahi Jatau inda kuma shugaban Hisbah na Jihar Kano Malam Daurawa ya kaddamar da ita.

▪︎Maigirma gwamna ya dawo da aikin Hisbah ne domin karfafa aiyukan gyaran tarbiyar al’umma a Jihar Sokoto, bisa koyarwar addinin Musulunci.

▪︎Domin tallafawa hukumar wajen gudanar da aiyukanta, an samar mata da motoci da babura da kuma wadataccen ofis. Kari akan wannan kuma, nan ba da dadewa ba, za a bude ofisoshin hukumar Hisbah na kananan hukumomi in sha Allah.

“Na bukaci sabuwar hukumar Hisban da ta tuna cewa, cin zarafin mutane da ba su ji ba kuma ba su gani ba, baya cikin dalilan da suka sa aka kafa ta. Na kuma umarci jami’an hukumar da su yi aiki bisa doron dokar da ta kafa hukumar, su kuma tabbatar da cewa aiyukansu ba su ci karo da kundin tsarin mulkin kasa ba.

Kafa hukumar Hisbah ba shi da manufar maye gurbin hukumomin tsaro da ake da su, sai dai za su tallafi harkar tsaro ne domin kare lafiya da dukiyoyin al’ummar Jihar Sokoto.

Jami’an hukumar za su yi aiki ne bisa doka, wacce ta basu damar yin kame, daga bisani su kuma mika wanda ake zargi ga jami’an ‘Yansanda domin gurfanar da shi a gaban kotun shari’ar musulunci.

Za mu cigaba da bibiyar aiyukan hukumar domin tabbatar da cewa sun bi shimfidaddun dokoki da ka’idoji wajen gudanar da aiyukansu.” – Dr. Ahmad Aliyu Sokoto FCNA

Shugaban AYSAS, Bashar Attahiru ya yi kira ga al’ummar Jihar Sokoto da su ba hukumar da jami’anta hadin kai wajen sauke nauyin da ya rataya akansu.

 

At’tajdid News

You Might Also Like

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

2025 World Sight Day: NOA Advocates Eye Healthcare Consciousness 

ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI

The 2009 ASUU Agreement and the FGN’s Endless Broken Promises

Attajdid May 21, 2025 May 21, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Dakarun Hadaka na ‘Yan Gwagwarmayar ‘Yantar da Kasar Palestine a Gaza Sun kai Wasu Jerin Hare-hare Ga ‘Yan Kama Wuri Zauna

Attajdid Attajdid August 1, 2025
Since 2012, there have been countless incidents of physical and verbal assaults against priests and other clergy, attacks on Christian churches
Gwamnatin Taliban ta Halarci Taron MDD Karo na Farko a Azabaijan
YAHUDAWAN SAHYONIYYA SUNA KASARA MAKOMAR ILIMI A GAZA.
Emir Sunusi, , Governors,, PDP Leaders, Civil Society, Advisers Console Jigawa Governor 
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?