By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > Uncategorized > ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI
Uncategorized

ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI

Attajdid
Last updated: 2025/09/03 at 7:38 AM
Attajdid Published September 3, 2025
Share
SHARE

ZANGA-ZANGA A SOKOTO: JAMA’A NA KUKAN TSARO, GOMNATI NA DAUKAR SABON MATAKI

 

A jihar Sokoto, Arewa maso Yammacin Najeriya, al’umma sun gudanar da zanga-zanga kan matsalar tsaro da ta addabi yankunansu. Mazauna kauyuka sun bayyana cewa a tsawon kwanaki uku a jere, ‘yan bindiga sun rika kai hare-hare tare da sace mutane ba tare da jami’an tsaro sun kawo dauki ba.

 

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa: “Rashin kulawar da gwamnati ta nuna mana ya sa muka rufe hanyar mota don janyo hankalinta da jami’an tsaro.”

 

A yayin da ake cikin wannan hali, wasu al’ummar yankin sun yi ikirarin cewa gwamnatin jiha ta yi watsi da su, inda wasu mata suka bayyana irin asarar da suka yi sakamakon hare-haren. Wata mata mai suna Tunba ta ce ta rasa ‘ya’yanta guda biyar, tana mai rokon gwamnati ta samar musu da tsaro.

 

Hukumomin NEMA da SEMA sun tabbatar da cewa sun riga sun san da lamarin, inda daruruwan mutane suka tsere daga gidajensu suna neman mafaka a yankin Shagari. Hakiman kauyukan da abin ya shafa kuma sun roki gwamnati ta kawo daukin gaggawa domin a dawo da zaman lafiya.

 

A wani labarin makamancin haka, wani hatsarin kwale-kwale ya rutsa da mutanen da ke kokarin tserewa ‘yan bindiga a karamar hukumar Sabon Birni. Rahotanni sun tabbatar da mutuwar mutane shida, yayin da wasu kuma suka bace cikin ruwa.

 

A gefe guda kuma, gwamnatin jihar ta sanar da wani shirin tallafawa koyar da addinin Musulunci da kuɗin alawus na N500,000 da za a rika biyan malamai a wasu yankuna. Wannan mataki ya samu yabo daga Sarkin Musulmi da sauran shugabanni, inda suka ce zai taimaka wajen karfafa zaman lafiya da haddar Alkur’ani a tsakanin matasa.

 

Rahoto: M.B.S.Gama

You Might Also Like

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

TRUMP AND CHRISTIAN GENOCIDE IN NIGERIA

2025 World Sight Day: NOA Advocates Eye Healthcare Consciousness 

The 2009 ASUU Agreement and the FGN’s Endless Broken Promises

Gwamnatin tarayya ta cire sama da naira biliyan 256 daga rabon kudaden man fetur na wata-wata, a kashi na farko na rabin shekarar 2025 domin aiwatar da ayyukan gine-ginen bututun gas a faɗin ƙasar nan.

Attajdid September 3, 2025 September 3, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

SPEED ACTION TO END INSECURITY IN ZAMFARA, NORTH-WEST– PRESIDENT TINUBU CHARGES TROOPS

Attajdid Attajdid October 25, 2024
WACECE JANNA JIHAD ❓
Kungiyar Jama’atut Tajdidil Islamy (JTI) Yankin Kano ta Gabas ta Gabatar da Taron Karawa Juna Sani Akan Tarbiyya da Shaye-shaye Kayan Maye
A Massive Database of Evidence, Compiled by a Historian, Documents Israel’s War Crimes in Gaza
Zenith Bank Donates N50 Million to Victims Of Jigawa Tanker Explosion 
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?