Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce mutane biyu sun mutu a wani harin da aka kai a wani gari a arewacin Isra’ila
Kafofin yada labaran Isra’ila sun ce mutane biyu ne suka mutu a wani hari da aka kai kan Majd al Krum a arewacin Isra’ila, bayan wata sanarwar da kungiyar Hezbollah ta fitar ta ce ta kai hari kan garin Karmiel da ke arewacin Isra’ila da wani babban makami mai linzami.
Kungiyar Hezbollah ta ce ta kai hari kan wata tankar yaki ta Merkava na Isra’ila a wajen garin Marwahin da ke kudancin kasar Lebanon, lamarin da ya yi sanadin mutuwar wani ma’aikacin jirgin tare da jikkata wani.
Kazalika tankar ta kama da wuta bayan da harin makami mai linzami ya same ta.
Kungiyar ta kuma ta harba rokoki a yankin Karmiel a arewacin Isra’ila.
Isra’ila ta kashe aƙalla mutum 2,574 a hare-hare a Lebanon.
At-tajdid News.




