By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Yan Nigeria sun koka akan barazanar da suke fuskanta a African ta kudu
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Yan Nigeria sun koka akan barazanar da suke fuskanta a African ta kudu
News

Yan Nigeria sun koka akan barazanar da suke fuskanta a African ta kudu

Attajdid
Last updated: 2025/09/13 at 3:37 PM
Attajdid Published September 13, 2025
Share
SHARE

‘Yan Nigeria da ke zaune a kasar Afirka ta Kudu sun koka da yadda su ke fama da Barazana da kuma Kyama daga Kungiyar nan da ta yi Kaurin suna wajen Kyamar ‘Yan cirani wato ‘Operation Dudula’.

Shugaban Kungiyar ‘Yan Nigeria mazauna kasar Afirka ta Kudu Frank Onyekwelu ya bayyana hakan inda ya yi kira da a gaggauta daukar matakan diflomasiyya a sakamakon rahoton hare-hare da cin zarafi da Kungiyar ta a fatattaki ‘Yan cirani ta ke musu da kuma yadda su ka haramtawa ‘Yan kasashen ketare amfana da Asibitocin kasar ta Afirka ta Kudu.

A cewar rahotanni koken na ‘Yan Nigeria na da nasaba da yadda tun a farkon shekarar nan su ka yi fama da kyama daga Kungiyar da kuma yadda a halin yanzu su ke cike da fargabar bullar wani sabon salon kyama da kuma hantara daga Kungiyar ta a Kori ‘Yan cirani.

A wani fefen Bidiyo da ya karade dandalin sada zumunta an ga yadda shuwagabannin Kungiyar ta a fatattaki ‘yan cirani a Afirka ta kudu su ka yi ta ba da umarnin a kori ‘Yan cirani daga Asibitocin kasar.

Shugaban Kungiyar ta ‘Yan Nigeria mazauna kasar Afirka ta kudu Frank Onyekwelu ya koka da yadda aka fara samun mata masu juna biyu daga cikin ‘Yan cirani a Afirka ta kudu da su ka fara haihuwa a dandariyar siminti ba tare da samun kulawar likitoci ba, da kuma yadda Asibitocin kasar su ke sallamar majinyata ba tare da ba su kulawa ba.

A cewar rahotanni ‘Yan kungiyar ta Dudula da ke rajin a fatattaki ‘Yan cirani daga kasar ta Afirka ta kudu sun yi ikirarin cewa su na yaki ne da masu shiga kasar ba bisa ka’ida ba, da masu safarar kwaya da kuma masu mamaye guraben aiyukan yi da ya kamata al’ummar kasar su amfana da su.

Mai Rahoto

Nura Abubakar Musa

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid September 13, 2025 September 13, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Hare-hare Suna Kara Zafafa Tsakanin Dakarun Mukawama ”yan Kasa da Yahudawan Sahyoniyawan ‘Yan Kama Wuri Zauna a Gaza

Attajdid Attajdid August 15, 2025
Musulmin Duniya Za Su Yi Duk Mai Yuwa Domin Kare Masallacin Qudus Mai Alfarma Tare Da Gargadin Firaministan Isra’ila NetanyahuFidan ya gargadi masu goyon bayan firaministan Isra’ila Netanyahu.
Gov Yusuf emerges SME Governor of year 2024
Dalilin da ya Hana ni Zuwa Kano Tarbar Tinubu: Ganduje
Yahudawan Sahyoniyya Sun Kai Jiran Hare-hare Sama da Ashirin (20) a Gaza
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?