‘Yan Nigeria da ke zaune a kasar Afirka ta Kudu sun koka da yadda su ke fama da Barazana da kuma Kyama daga Kungiyar nan da ta yi Kaurin suna wajen Kyamar ‘Yan cirani wato ‘Operation Dudula’.
Shugaban Kungiyar ‘Yan Nigeria mazauna kasar Afirka ta Kudu Frank Onyekwelu ya bayyana hakan inda ya yi kira da a gaggauta daukar matakan diflomasiyya a sakamakon rahoton hare-hare da cin zarafi da Kungiyar ta a fatattaki ‘Yan cirani ta ke musu da kuma yadda su ka haramtawa ‘Yan kasashen ketare amfana da Asibitocin kasar ta Afirka ta Kudu.
A cewar rahotanni koken na ‘Yan Nigeria na da nasaba da yadda tun a farkon shekarar nan su ka yi fama da kyama daga Kungiyar da kuma yadda a halin yanzu su ke cike da fargabar bullar wani sabon salon kyama da kuma hantara daga Kungiyar ta a Kori ‘Yan cirani.
A wani fefen Bidiyo da ya karade dandalin sada zumunta an ga yadda shuwagabannin Kungiyar ta a fatattaki ‘yan cirani a Afirka ta kudu su ka yi ta ba da umarnin a kori ‘Yan cirani daga Asibitocin kasar.
Shugaban Kungiyar ta ‘Yan Nigeria mazauna kasar Afirka ta kudu Frank Onyekwelu ya koka da yadda aka fara samun mata masu juna biyu daga cikin ‘Yan cirani a Afirka ta kudu da su ka fara haihuwa a dandariyar siminti ba tare da samun kulawar likitoci ba, da kuma yadda Asibitocin kasar su ke sallamar majinyata ba tare da ba su kulawa ba.
A cewar rahotanni ‘Yan kungiyar ta Dudula da ke rajin a fatattaki ‘Yan cirani daga kasar ta Afirka ta kudu sun yi ikirarin cewa su na yaki ne da masu shiga kasar ba bisa ka’ida ba, da masu safarar kwaya da kuma masu mamaye guraben aiyukan yi da ya kamata al’ummar kasar su amfana da su.
Mai Rahoto
Nura Abubakar Musa




