Ghana ta kama baƙin haure 2,000 a ƙoƙarinta na yaƙi da bara a ƙasar
Hukumomi a ƙasar Ghana sun sanar da kama baƙin haure aƙalla guda 2,000 a ƙoƙarin da gwamnatin ƙasar ta ce tana yi domin yaƙi da barace-barace a titunan ƙasar, musamman a babban birnin ƙasar, Accra, kamar yadda kafar Joy Online mai zaman kanta a ƙasar ta ruwaito.
“Yanzu haka suna tsare ana tantance su,” in ji hukumar kula da baƙin haure ta ƙasar.
Ta ƙara da cewa daga cikin waɗanda aka kama akwai ƙananan yara guda 1,332, waɗanda hukumar ta ce za a ba su kula ta musamman domin kare haƙƙinsu.
Ministan harkokin cikin gida na ƙasar, Muntaka Mubarak ya ce sun gudanar da kamen ne “domin yaƙi da barace-barace a titunan ƙasar,” in ji shi, wanda ya ƙara da cewa har da baƙin haure.
Ya ce yawancin waɗanda aka kama ɗin sun shigo Ghana ta ɓarauniyar hanya ce, “kuma suna barazana ga zaman lafiyar ƙasar.”
Ya ce yawancin waɗanda aka kama ɗin ƴan ƙasashen Togo da Burkina Faso da Najeriya ne.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




