Wata mota da ta kwace ta faɗa cikin dandazon jama’a a kofar cibiyar wasanni da ke Kudancin China ta yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutane 35.
Sannan wasu 43 kuma sun jikkata a lamarin da ya faru ranar Litinin a cewar hukumomi.
Shugaba Xi ya yi kira da a hukunta wanda ya haifar da hatsarin motar.
Kafofin yaɗa labaran China sun ruwaito cewa cikin mutanen da suka jikkata sun haɗa da tsofaffi da matasa da kuma yara.
Ƴansanda sun ce sun kama wani yayin da yake ƙoƙarin tserewa, kuma yana cikin dogon suma sakamakon raunuka da ya ji.
Lamarin ya faru duk da irin tsauraran matakan tsaro a birnin, wanda ke karɓar bakuncin wani bikin jama’a da kuma na sojoji.
Ƴansanda sun ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa haɗarin ya afku ne sakamakon ɓacin rai da wani magoyin bayan kwallon kafa ya yi, saboda an raba dukiyarsa bayan ya saki matarsa.
Sai dai saboda da dogon suma da ya shiga, hukumomi ba su samu damar yi masa tambayoyi ba.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu




