By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Gwamnatin Tarayya Zata Sabunta Tsarin Koyarawa A Makarantu Da, Jami’oi
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Gwamnatin Tarayya Zata Sabunta Tsarin Koyarawa A Makarantu Da, Jami’oi
News

Gwamnatin Tarayya Zata Sabunta Tsarin Koyarawa A Makarantu Da, Jami’oi

Attajdid
Last updated: 2025/09/01 at 9:26 PM
Attajdid Published September 1, 2025
Share
SHARE

Gwamnatin Tarayya Zata Sabunta Tsarin Koyarawa A Makarantu Da, Jami’oi

 

Gwamnatin Tarayya ta kammala cikakken bitar manhajar makarantu na matakin firamare, sakandire da kuma na makarantun koyar da ilimin sana’o’i domin dora ɗaliban Najeriya a kan shirin da zai zamo daidai da buƙatunsu na gaba.

 

A cikin sanarwar da ma’aikatar ilimi ta fitar ta hannun daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na ma’aikatar, Boriowo Folasade, da ya sanya wa takardar hannu a ranar Juma’a, aka kuma rabawa manema labarai.

 

Folasade ya ce karamar ministan ilimi, Farfesa Suwaiba Ahmad, ce ta sanar da manhajar a madadin ministan ilimi, Dakta Tunji Alausa, yayin da take jawabi a birnin Abuja.

 

A cewar ministar, an gudanar da wannan bita ne tare da haɗin gwiwar manyan masu ruwa da tsaki a harkar ilimi, ciki har da hukumar bincike da ci gaban ilimi ta Najeriya NERDC da hukumar ilimin bai daya UBEC da hukumar ilimin Sakandire ta ƙasa NSSEC da kuma hukumar ilimin fasaha NBTE.

 

Sabon tsarin manhajar an tsara shi ne domin rage cunkoson a harkokin koyo da koyarwa, inganta sakamakon koyon ilimi, tare da tabbatar da cewa ɗaliban Najeriya suna samun ƙwarewar da ta dace da bukatun duniya na zamani.

 

 

Ƙarkashin sabon tsarin, ɗaliban aji daya zuwa 3 na Firamare za su yi karatu da darussa mafi ƙanƙanta daga 9 zuwa 10; yayin da ɗaliban aji 4 zuwa 6 na Firamare za su ɗauki darussa 10 zuwa 12.

 

Su kuwa ɗaliban karamar Sakandire za su ɗauki darussa 12 ne zuwa 14, sai kuma ɗaliban babbar Sakandire da za su yi darussa 8 zuwa 9, sannan ɗaliban makarantu na fasaha za su ɗauki darussa 9 zuwa 11.

 

Ma’aikatar ba ta bayyana takamaiman ranar da za a fara amfani da sabbin manhajojin ba, amma ta ce za a gabatar da su a hankali tare da kulawa daga hukumomin da abin ya shafa domin tabbatar da an aiwatar da su yadda ya kamata.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid September 1, 2025 September 1, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
NewsUncategorized

FG, FMAN Supports 160,000 Wheat Farmers In Jigawa

Attajdid Attajdid February 19, 2025
Takaitattun labarai Daga Jenin Da Gaza Da Kuma Lebanon
Emir of Rano bags Honorary Doctorate Degree of Excellence 
Idan Isra’ila Ta Samar da Iron Dome Turkiyya Zata Samar da Steel Dome, (Rumfar Ƙarfe)” Inji Shugaba Erdogan
Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?