Bayanan hoto,Alexander Troufanov da Yair Horn da kuma Sagui Dekel-Chen duk suna cikin mutanen da mayaƙan Hamas suka kwasa daga Isra’ila a ranar da suka kai samame
Hamas ta saki sunayen mutum uku da take garkuwa da su waɗanda za ta saki gobe Asabar domin yin musaya da Falasɗinawan da Isra’ila ke riƙe da su a wani ɓangare na ci gaba da aiwatar da yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin biyu.
Hakan na zuwa ne bayan kwanakin da aka kwashe ana fargabar wargajewar yarjejeniyar.
Isra’ilawan da za a sakin su ne: Alexander Troufanov – ɗan Isra’ila mazaunin Rasha, da Yair Horn – ɗan Isra’ila mazaunin Argentina, da kuma Sagui Dekel-Chen – ɗan Isra’ila mazaunin Amurka.
Isra’ila ta bayyana cewa za ta ci gaba da ruwan wuta a kan Gaza idan ba a saki mutanen a kan lokaci ba.
Taƙaddama ta kaure ne bayan da Hamas ta yi barazanar dakatar da sakin mutanen na Isra’ila bayan zargin Isra’ilar da karya ƙa’idojin yarjejeniyar tsagaita wuta.
Tun bayan fara aiki da yarjejeniyar tsagaita wutar a ranar 19 ga watan Janairu, Hamas ta saki Isra’ilawa 16, da ƴan ƙasar Thailand biyar yayin da ita kuma Isra’ila ta saki Falasɗinawa 566 da take riƙe da su a gidajen yarinta.
Ana sa ran Hamas za ta saki ‘ƴan Isra’ila 33 da take garkuwa da su a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar, yayin da ita kuma Isra’ila za ta saki Falasɗinawa 1,900.
Yaƙi ya turnuƙe a Gaza ne tun bayan da Hamas ta kai wani hari kan Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoban 2023, inda mayaƙanta suka kashe kimanin mutum 1,200 tare da yin garkuwa da wasu mutum 251.
Tun bayan wancan lokacin, ma’aikatar lafiya ta Hamas ta ce an kashe sama da mutum 48,230 sanadiyyar luguden wuta da Isra’ila ta riƙa yi a Gaza. BBC Hausa.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




