By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Isra’ila Tana Luguden Wuta ta Sama a Beirut Bayan da take Fama da Wata Mummunar Tarjiya daga Dakarun Hezbollah
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Isra’ila Tana Luguden Wuta ta Sama a Beirut Bayan da take Fama da Wata Mummunar Tarjiya daga Dakarun Hezbollah
International News

Isra’ila Tana Luguden Wuta ta Sama a Beirut Bayan da take Fama da Wata Mummunar Tarjiya daga Dakarun Hezbollah

Attajdid
Last updated: 2024/10/03 at 8:48 AM
Attajdid Published October 3, 2024
Share
SHARE
  1. Isra’ila ta kai harin bam a tsakiyar birnin Beirut da sanyin safiyar Alhamis, inda ta kashe akalla mutane shida, bayan da sojojinta masu mamaya suka ga mafi munin rana a gagarumin artabun da ba su taba irinsa ba a fagen daga tsakaninsu da kungiyar Hezbollah ta Lebanon a cikin shekara guda.
  2. Shaidu sun ba da rahoton jin karar fashewar wani katon bam kuma wata majiyar tsaro ta ce Isra’ila ta kai hari kan wani gini da ke tsakiyar birnin Beirut a unguwar Bachoura da ke kusa da majalisar dokokin kasar, harin da Isra’ila ta kai a kusa da ofishin gwamnatin Lebanon.
  3. Akalla mutum shida ne suka mutu sannan bakwai suka jikkata, in ji jami’an kiwon lafiya na kasar Lebanon.
  4. Wani hoto da ake yadawa a kafofin WhatsApp a kasar Lebanon ya nuna wani gini da ya lalace sosai tare da cin wuta a benensa na farko.
  5. Har ila yau, sun kai harin makami mai linzami uku a yankin kudancin Dahiyeh, inda aka kashe shugaban kungiyar Hezbollah Hassan Nasrallah a makon da ya gabata, an kuma ji karar fashewar wasu abubuwa masu karfi kamar yadda jami’an tsaron kasar Labanon suka sanar.
  6. Yankunan kudancin kasar sun fuskanci hare-hare sama da goma na Isra’ila a ranar Laraba.
  7. Hukumar kula da bala’o’i ta kasar Lebanon ta fada a baya cewa mutane 1,928 Isra’ila ta kashe a kasar tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.
  8. Gwamnatin Amurka ta ce an kashe wani Ba’amurke dan asalin garin Dearborn a jihar Michigan, a kasar Labanon, inda abokin mutumin da makwabtansa suka ce an kashe shi ne a wani harin da Isra’ila ta kai ta sama.
  9. Kakakin Fadar White House ya ce “Muna matukar bakin ciki da rasuwar Kamel Ahmad Jawad, kuma muna mika ta’aziyyarmu ga ‘yan uwansa da abokan arziki. Mutuwar tasa wata abar takaici ce, haka ma mutuwar fararen hula da dama a Lebanon.”
  10. Tun da farko dai, kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, da aka tambaye shi game da rahotannin mutuwar wani Ba’amurke a Lebanon, ya ce: “A fahimtarmu ne cewa mazaunin kasar ne na dindindin bisa tsarin doka, ba wani Ba’amurke ba (wanda aka kashe a Lebanon) amma duk da haka muna mika ta’aziyyarmu ga ‘yan uwa.”
  11. Yakin da Isra’ila ke yi a Zirin Gaza, wanda yanzu ya shiga kwana na 363, ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa akalla 41,638. Bugu da ƙari, sama da mutane 1,928 ne suka mutu a wani munanan hare-haren da Isra’ila ta kai a Lebanon.
  12. At-tajdid News.

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid October 3, 2024 October 3, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

An Sami Tirjiya Mai Tsanani Tsakanin Dakarun Hezbollah da sojojin Isra’ila  a Lebanon

Attajdid Attajdid October 22, 2024
Ana Cigaba Kashe ‘Yan Jaridu a Gaza Sakamakon Harin Yahudawan Sahyoniya a Gaza
Sarkin Musulmi ya Bayyana Dalilin da ya sa Ake Ganin Kamar Sarakuna na Tsoron Gwamnoni
SHEKARU 64 DA SAMUN ‘YANCI
Haɗarin Babbar Mota ya yi Ajalin Mutum 16 a Kano
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?