Mayakan Hezbollah sun gwabza kazamin fada da sojojin kasa na Isra’ila a kan iyakokin kasar guda uku a kudancin kasar Lebanon, kamar yadda kafafen yada labaran kasar Labanon suka bayyana.
Kafar yada labaran ta ce sojojin Isra’ila sun yi luguden wuta kan Aita al-Shaab, Qaouzah da Ramiya da manyan bindigogi.
A gefe guda kuma, wata yarinya ‘yar kasar Lebanon ta mutu sakamakon raunukan da ta samu a wani harin da jiragen yakin Isra’ila suka kai a garin Kharayeb da ke gabashin kasar Lebanon, kamar yadda NNA ta ruwaito.
An kuma bayar da rahoton wasu hare-hare ta sama da dama a garuruwan Kharayeb, Houmine El Faouqa, Jarjouaain, Habbouch da kuma Arab Salim da ke kudancin kasar Lebanon.
Lebanon ta ce harin da Isra’ila ta kai a babban birnin Baalbek da ke gabashin kasar ya kashe mutum shida ciki har da wani yaro, yayin da kafafen yada labarai na kasar suka rawaito cewa harin ya afkawa wani gini da ke wani yanki mai cike da cunkoso.
“Harin da makiyanmu Isra’ila suka kai…a Baalbek ya kashe mutane shida, ciki har da wani yaro,” in ji ma’aikatar lafiya ta kasar Lebanon, kuma kamfanin dillancin labaran kasar ya ruwaito cewa dukkan mutanen shida ‘yan gida daya ne.
At-tajdid News.




