By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Zulum ya jaddada kudirinsa na sake tsugunar da wadanda rikicin Boko Haram ya shafa
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Zulum ya jaddada kudirinsa na sake tsugunar da wadanda rikicin Boko Haram ya shafa
News

Zulum ya jaddada kudirinsa na sake tsugunar da wadanda rikicin Boko Haram ya shafa

Attajdid
Last updated: 2024/11/27 at 7:31 PM
Attajdid Published November 27, 2024
Share
SHARE

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya jaddada kudirin gwamnatinsa na sake tsugunar da wadanda rikicin Boko Haram ya shafa cikin mutunci da tsari mai dorewa.

 

Gwamnan ya yi wannan alkawarin ne a yayin ziyarar ban girma da ministan harkokin jin kai da yaki da fatara, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, ya kai masa ranar Talata a fadar gwamnati dake Maiduguri.

 

Da yake jawabi a ci gaba da kalubalan da ‘yan gudun hijirar ke fuskanta, Gwamna Zulum ya jaddada cewa tallafin da kungiyoyi na kara tsukewa, shi yasa akwai bukatan tsugunar da jama’a maikokon cigaba da zama a sansanonin ‘yan gudun hijira.

 

“Masu gudun hijira sun dade da yawa a sansanonin; Muna son su tashi su sami abin rayuwarsu. Yayin da kungiyoyin Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyi masu zaman kansu suna aiki abin yabawa, babu wani ci gaba da bayar da kudade don ciyar da mutane a wadannan sansanonin,” in ji Zulum.

 

Gwamnan ya jaddada bukatar samar da tsari mai dorewa don magance kalubalen jin kai da suka hada da sake tsugunar da mutanen da suka rasa matsugunansu.

 

Ya yi alkawarin hada kai da hukumomi da ke karkashin ma’aikatar jin kai don gaggauta dawo da ‘yan gudun hijirar cikin aminci da mutunci.

 

A jawabin sa, Ministan Harkokin Agaji, Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda, ya sanar da shirye-shiryen ma’aikatar don sanya tsarin jin kai na Borno cikin cikakken Tsarin Ba da Agajin Gaggawa na kasa.

 

Ya yabawa Gwamna Zulum kan yadda ya mayar da hankali wajen dawo da gyare-gyare, da kokarin sake ginawa, wadanda suka kasance masu muhimmanci wajen dawo da ababen more rayuwa da kuma farfado da rayuwar al’umma a jihar.

 

“Gwamna Zulum ya bayar da jagoranci na kwarai ta hanyar daidaita kokarin jihar da abokan huldar kasa da kasa, tare da tabbatar da cewa a hankali ayyukan rayuwa da zamantakewa suna komawa Borno,” in ji Ministan.

 

Ministan ya kuma bayyana shirin mayar da ‘yan gudun hijirar Najeriya zuwa garuruwan su, tare da yin alkawarin ba su damar dogaro da kai.

 

Ministan ya samu rakiyar kwamishinan tarayya, hukumar kula da ‘yan gudun hijira, da bakin haure, Hon. Tijani Aliyu Ahmed, babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan shirin ciyar da dalibai, Dr. Yetunde Adeniji, tare da manyan jami’an ma’aikatar.

 

Dauda Iliya

Mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Borno

(Kan yada labarai/Mai magana da yawun sa)

 

 

Mai rahoto;

Abdullahi Mustapha.

 

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid November 27, 2024 November 27, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

YARA MANYAN GOBE: A RANAR YARA TA DUNIYA DAGA FADAR SARKIN KATSINAN GUSAU, ALH. DR. IBRAHIM BELLO.

Attajdid Attajdid November 22, 2024
Global hunger hits new high amid conflict, extreme weather: UN
Real Madrid ta amince da biyan Fam Miliyan 50 ga Dan wasa Dean Huijsen
Tafsir rana(2) 1445 Malam Aminu Aliyu Gusau (moddiban gusau)da Alaramma Yushe’u sani kwanar ganuwa.
TA’AZIYYA DA JAJANTAWA GA MUTANEN MAIDUGURI DAGA ALKALI SANUSI MUHAMMAD MAGAMI
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?