‘Yan kama-wuri-zauna huɗu a Daidai Lokacin Da Al’amuru Suke Kara RincabewaA rana ta 330 da Isra’ila ta kwashe tana yaƙi a Gaza, ta kashe Falasɗinawa aƙalla 40,602 galibinsu mata da yara tare da jikkata fiye da 93,855, inda hasashe ya bayyana sama da mutum 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzan gidajen da aka yi wa ruwan bam.
Gawawwakin Falasɗinawa, ciki har da jarirai waɗanda aka kashe a harin da Isra’ila ta kai Sansanin ‘Yan Gudun Hijira na Nuseirat, da akai kai ɗakin ajiye gawawwaki na Asibitin Shahidai na Aqsa a Deir Sojojin Isra’ila sun kashe Falasɗinawa 12 a jerin hare-hare a yankin Gaza da aka mamaye, yayin da aka zaƙulo wasu gawawwaki daga wuraren da sojojin Isra’ila suka bari, da suka yi ka-ka-gida a baya.Mai magana da yawun Cibiyar Kare Fararen-Hula ta Falasɗinawa Mahmoud Basal ya bayyana cewa an kashe Falasɗinawa shida a wasu hare-haren Isra’ila biyu ta sama a Jabalia da ke arewacin Gaza, ciki har da wani hari da aka kai wa wani taron mutane.
A unguwar Sheikh Radwan da ke arewa maso yammacin Birnin Gaza kuwa, an kashe wani Bafalasɗine a harin jirgin saman Isra’ila a wani gida da ake zama, kamar yadda sanarwar ta bayyana.A tsakiyar Gaza ma, an kashe Falasɗinawa biyu a wani hari ta sama kan wani gida a sansanin ‘yan gudun hijira na Al-Maghazi da kuwa wani wajen da jama’a suka taru a Deir al-Balah.A Khan Younis kuma, Falasɗinawa uku aka kashe a wani hari ta jirgin yaƙi a kan wani gida a garin Abasan al-Kabira, a gabashin Khan Younis.
An jikkata Yahudawa ‘yan kama-wuri-zauna a Gaɓar Yamma an jikkata aƙalla Isra’ilawa ‘yan kama-wuri-zauna huɗu a wasu hare-hare daban-daban a haramtattun matsugunai na Gush Etzion a kudancin Gaɓar Yamma da Kogin Jordan da aka mamaye.
Kafofin watsa labaran Isra’ila sun ba da rahoton cewa sojojin Isra’ila sun kashe waɗanda suka kai harin.
Gidan Rediyon Sojojin Isra’ila ya ba da rahoton cewa wasu ‘yan kama-wuri-zauna biyu sun ji rauni yayin da wani bam da aka sa a mota ya tashi a Gush Etzion; ɗaya ya ji rauni matsakaici, yayin da ɗayan kuma ya ji rauni kaɗan.
At-tajdid News.




