An gurfanar da mutum 47 a gaban kotu a Turkiyya bisa zargin hannu a wata badaƙala ta sauya wa jarirai sababbin haihuwa asibitoci domin samun kuɗi.
Masu gabatar da ƙara sun ce likitoci da ma’aikatan jinya da direbobin motocin ɗaukar marassa lafiya sun haddasa mutumawr aƙalla jarirai goma a sanadiyyar badaƙalar.
Ana zargin mutanen ne da bayar da bayanan ƙarya na rashin lafiyar jarirai domin sauya wa jarirai 19 asibiti daga na gwamnati zuwa na ‘yan kasuwa, inda ake ajiye su wajen kulawar gaggawa tsawon lokacin a kan yi musu maganin da bai zama wajibi ba.
Takardar tuhumar ta nuna cewa waɗanda ke da hannu a cuwa-cuwar suna raba kuɗin da ake bayarwa daga shirin tallafi na gwamnati, da ake biya kullum na kwanan jariri a asibitin.
Mutane sun musanta zargin da ake yi musu da cewa duk abin da suka yi sun yi ne domin ceto ran jariran
Idan aka same su da laifi za a iya yanke musu hukuncin ɗauri mai tsawo a kan laifin kisan kai ta hanyar sakaci da zamba da kuma ƙarya.
‘Yansanda sun ƙaddamar da bincike ne bayan da aka tsegunta musu badaƙalar a watan Maris na 2023, lamarin da da ya kai ga soke lasisin asibiti goma.
Mai Rahoto;
Mujahid Muhammad Tasiu.
At-tajdid News.




