Uwargidan shugaban kasa sanata Oluremi Tinubu, ta kaddamar da sabbin na’urorin gano cutar tarin fuka da aka kera a wani mataki na saurin gano cutar a fadin kasar nan.
Rahotanni dai na nuni da Najeriya ce kasar da ta fi kowacce yawan cutar tarin fuka a Afirka, kuma ana samun sabbin masu kamuwa da tarin fukar kusan 350,000 duk shekara a kasarnan.
Sabbin Injinan gano cutar tarin fuka na iya ganowa da kuma samar da sakamakon gwaji a cikin ƙasa da mintuna 30.
A saboda haka, Uwargidan Shugaban kasar ta yi kira ga masu ruwa da tsaki da su kara himma wajen ganin Najeriya ta kawo karshen cutar tarin fuka nan da shekarar 2030.
Da yake jawabi a wurin kaddamar da injinan a jiya a birnin tarayya Abuja, Tinubu ya lura cewa, duk da cewa cutar tarin fuka na iya warkewa, har yanzu ‘yan Najeriya da dama na mutuwa saboda cutar saboda babu fasahar gano cutar, da kuma takaita hanyoyin yin amfani da na’urorin tantance cutar da suka dace.
Hakanan, a wani muhimmin mataki na samar da cigaban fannin lafiya a kasarnan, Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Asibitin Renewed Hope Mother and Child Specialist Hospital mai dauke da gadaje 100 a Oko-Ita dake karamar hukumar Ibiono Ibom ta jihar Akwa Ibom.




