A yau, Firayim Ministan Pakistan ya bayyana cewa yarjejeniyar da ta kawo ƙarshen kisan kiyashi a Gaza tana zama dama ta tarihi don samar da zaman lafiya na dindindin a Gabas ta Tsakiya.
Ya yaba da jagorancin Shugaba Donald Trump a tattaunawar, yana mai cewa hakan ya nuna jajircewarsa ga zaman lafiya ta duniya.
Haka kuma ya gode wa Qatar, Masar da Turkiyya bisa ƙoƙarinsu na cimma wannan yarjejeniya, tare da bayyana cewa Pakistan za ta ci gaba da aiki da ƙasashen abokai don tabbatar da zaman lafiya ga al’ummar Falasɗinu.
A Isra’ila kuwa, Gidan Rediyon Sojin Isra’ila ya ruwaito cewa rundunar da ke Gaza ta samu umarni da ta shirya don janyewa gaba ɗaya ko koma baya a cikin ’yan kwanaki masu zuwa.
A gefe guda, Ƙungiyar Jihadi al-Islami ta ce ceasefire da musayar fursunoni da aka cimma ba kyauta ba ce, sai dai ta yaba da ƙoƙarin ƙasashen Larabawa da na duniya.
Ƙungiyar ta jaddada cewa tashen hankali da jajircewar mayakanta ne suka bai wa Palasɗinu ƙarfi a teburin tattaunawa.
A nata bangaren kuma, Ministan Harkokin Wajen Italiya ya bayyana farin cikinsa da yarjejeniyar, yana mai cewa ƙasarsa na shirye ta tura dakarun wanzar da zaman lafiya idan aka kafa ƙungiyar kasa da kasa don taimaka wa Gaza.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




