Ministan tsaron Najeriya ya ce ƙasar ta samu dukkan cancantar da ake buƙata ta samun zama mamba a Kwamatin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD).Da yake gabatar da jawabi yayin wani taro a birnin New York na Amurka, Mohammed Badaru ya ce Najeriya ta ba da gudummawar kiyaye zaman lafiya a ƙasashe 41 tare da tura dakaru sama da 200,000.
Taron mai taken “Enhancing Multilateralism for International Peace and Security” game da zaman lafiya a duniya, wani ɓangare ne na taron babban zauren MDD na 76 da ake yi a Amurkar.
Tun daga fara tura dakarunmu a ƙasar Kongo a shekarar 1960, Najeriya ta shiga ayyuka 41 na kiyaye zaman lafiya a duniya,” in ji shi.
Ministan ya kuma nemi a yi gyara a tsarin kwamatin domin bai wa nahiyar Afirka kujerar wakilci ta dindindin.
Yanzu haka ƙasashen Amurka, da Birtaniya, da China, da Faransa, da Rasha ne kaɗai ke da wannan matsayin.
Mai rahoto;Salihu Garba.
At-tajdid News.




