“Dakarun mamaya sun yi wa Falasɗinawa hudu ƙawanya; mata biyu iyayen wasu Falasɗinawa biyu da dakarun Isra’ila suka kashe a sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin ,” in ji kamfanin dillancin labaran na Falasɗinu.
A lokacin da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta shiga kwana na huɗu bayan Isra’ila ta kashe Falasɗinawa aƙalla 47,161 a yankin sannan mahukuntan Isra’ila sun ci gaba da kai farmaki a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.
Dakarun mamaya na Isra’ila sun sace Falasɗinawa aƙalla bakwai daga biranen Jenin da Jericho na Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, kamar yadda kamfanin dillancin WAFA ya ambato wasu majiyoyi suna tabbatawa.
“Dakarun mamaya sun yi wa Falasɗinawa huu ƙawanya; mata biyu iyayen wasu Falasɗinawa biyu da dakarun Isra’ila suka kashe a sansanin ‘yan gudun hijira na Jenin ,” in ji kamfanin dillancin labaran na Falasɗinu.
Dakarun Isra’ila sun kai samame a birnin Jericho, lamarin da ya kai ga arangama, a cewar WAFA, inda kamfanin labaran ya ƙara da cewa dakarun an Isra’ila sun sace matasa biyu a yankin Silwan na Birnin Ƙudus.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




