By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Dakarun Isra’ila Sun Kai Samame Gaɓar Yammacin Kogin Jordan a Yayin da Suka Mamaye Jenin
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > International News > Dakarun Isra’ila Sun Kai Samame Gaɓar Yammacin Kogin Jordan a Yayin da Suka Mamaye Jenin
International News

Dakarun Isra’ila Sun Kai Samame Gaɓar Yammacin Kogin Jordan a Yayin da Suka Mamaye Jenin

Attajdid
Last updated: 2025/01/23 at 1:19 PM
Attajdid Published January 23, 2025
Share
SHARE

Yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta shiga kwana na huɗu bayan Isra’ila ta kashe Falasɗinawa aƙalla 47,161 a yankin sannan mahukuntan Isra’ila sun ci gaba da kai farmaki a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.

 

Dakarun Isra’ila suna shirin shiga Jenin da ke Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, inda suak tsaya a ƙauyen Muqeibila ranar 22 ga Janairu, 2025.

 

 

 

Dakarun Isra’ila sun kai samame a sassa daban-daban na Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, a cewar wasu majiyoyi, a yayin da suka mamaye birnin Jenin.

 

Kamfanin dillacin labaran WAFA na Falasɗinu ya ruwaito cewa dakarun Isra’ila sun kutsa cikin garin Turmusayya da ke arewacin Ramallah, kuma sun mamaye wasu muhimman gine-ginen gwamnati.

 

A Jenin, dakarun Isra’ila sun shiga ƙauyen Fahma inda suka riƙa harba tiyagas kan mutane, lamarin da ya kai ga arangama a tsakaninsu.

 

A Bethlehem, dakarun Isra’ila sun kai samame a garin al-Khader, inda suka mamaye Hanyar Birnin Ƙudus zuwa Hebron sannan suka riƙa fesa barkonon-tsohuwa kan ‘yan kasuwa a cikin shagunansu, ko da yake ba a samu rahoton jikkata ba.

 

Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio ya yi magana da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu domin jaddada goyon bayan Amurka a gare su, sannan mutanen biyu sun tattauna game da Iran da kuma yahudawan Isra’ila da ake garkuwa da su a Gaza, a cewar Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka.

 

Wannan shi ne karon farko da Rubio ya yi magana da jami’an Isra’ila tun bayan da aka rantsar da Donald Trump ranar Litinin.

 

Trump da mutumin da ya gabace shi, tsohon shugaban ƙasa Joe Biden, sun bayyana goyon yaƙin kisan ƙare-dangin da Isra’ila take yi a Gaza.

 

Rubio ya bayyana muhimmancin matakin ” Amurka na ci gaba da goyon bayan Isra’ila a matsayin babban abin da Trump ya sanya a gaba,” in ji wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar.

 

Rubio ya shaida wa Netanyahu cewa Washington za ta ci gaba da goyon bayan Isra’ila “ba tare da gajiyawa ba” domin ganin an ceto sauran mutanen da aka yi garkuwa da su a Gaza.

 

“Kazalika Sakataren Harkokin Wajen ya miƙa fatansa na ganin an daƙile duk wata barazana da ke fitowa daga Iran da kuma tabbatar da zaman lafiya,” a cewar sanarwar.

 

A ya yin da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta shiga kwana na huɗu bayan Isra’ila ta kashe Falasɗinawa aƙalla 47,161 a yankin sannan mahukuntan Isra’ila sun ci gaba da kai farmaki a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.

 

 

Mai rahoto;

M.B.S.Gama.

 

 

At-tajdid News.

You Might Also Like

Mass Turnout As Jigawa Flagg-Off 2025 Polio Immunization Campaign Targets 1.5 Million Children 

ZAMFARA STATE MUSLIMS LEAGUE FOR PEACE AND DEVELOPMENT OPEN LETTER TO TRUMP AND THE U.S.A CONGRESS:

Israel Strategies For Dividing Gaza Intro Two Zone

⭕️ Reuters, citing European and American sources

Israila ta Rushe Gidajen Falasɗinawa a Gaza, ta ƙaddamar da Sabon Hari a Khan Younis

Attajdid January 23, 2025 January 23, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

LG Poll: Governor Namadi Receives Hundreds Of Decamped From PDP AND NNPP

Attajdid Attajdid September 17, 2024
Hare-hare Suna Kara Zafafa Tsakanin Dakarun Mukawama ”yan Kasa da Yahudawan Sahyoniyawan ‘Yan Kama Wuri Zauna a Gaza
{AMBALIYAR RUWA} MUTUM 129 SUN MUTU YAYIN DA SAMA DA 120 SUKA JIKKATA A NIJAR.
SPEED ACTION TO END INSECURITY IN ZAMFARA, NORTH-WEST– PRESIDENT TINUBU CHARGES TROOPS
Tafsrin Alqur’ani Mai Girma Na Malam Aminu Aliyu Gusau Yau 7 Ramadan 1441 Daidai Da 30 April 2020
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?