Gwamnatin Tarayya zata Kammala Gyara Hanyar Jirgin Kasa Abuja-Kaduna Cikin Kwanakinnan 10
Ministan Sufuri na ƙasa, Injiniya Said Ahmed Alkali, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa za a kammala gyaran hanyar jirgin ƙasa da ta lalace a layin Abuja zuwa Kaduna cikin kwanaki goma.
Wannan na zuwa ne bayan hadarin da wani jirgin ƙasa ya yi a tashar Asham a makon da ya gabata, inda wasu sassa na hanyar jirgin da kuma wasu ƙofofin jirgin suka lalace.
Jirgin dai na ɗauke da fassinjoji 583, tare da ma’aikata 35, ciki har da jami’in lafiya, Jami’an tsabta, da kuma masu kula da abinci.
Mutane bakwai ne suka samu raunuka a hadarin, amma ba a rasa rai ba.
Minista Alkali ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin da lamarin ya faru, inda ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro da ma’aikatan Hukumar Jirgin Ƙasa ta Ƙasa, wato NRC, wajen tabbatar da tsaron fasinjoji da kuma saurin mayar da hanyar ta koma aiki.
Ya ƙara da cewa ma’aikatan NRC na aiki dare da rana domin tabbatar da cewa ayyukan jirgin ƙasa sun dawo cikin ƙanƙanin lokaci.




