By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Gwamnatin Tarayya zata Kammala Gyara Hanyar Jirgin Kasa Abuja-Kaduna Cikin Kwanakinnan 10
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Gwamnatin Tarayya zata Kammala Gyara Hanyar Jirgin Kasa Abuja-Kaduna Cikin Kwanakinnan 10
News

Gwamnatin Tarayya zata Kammala Gyara Hanyar Jirgin Kasa Abuja-Kaduna Cikin Kwanakinnan 10

Attajdid
Last updated: 2025/09/03 at 11:39 AM
Attajdid Published September 3, 2025
Share
SHARE

Gwamnatin Tarayya zata Kammala Gyara Hanyar Jirgin Kasa Abuja-Kaduna Cikin Kwanakinnan 10

 

Ministan Sufuri na ƙasa, Injiniya Said Ahmed Alkali, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa za a kammala gyaran hanyar jirgin ƙasa da ta lalace a layin Abuja zuwa Kaduna cikin kwanaki goma.

 

Wannan na zuwa ne bayan hadarin da wani jirgin ƙasa ya yi a tashar Asham a makon da ya gabata, inda wasu sassa na hanyar jirgin da kuma wasu ƙofofin jirgin suka lalace.

 

Jirgin dai na ɗauke da fassinjoji 583, tare da ma’aikata 35, ciki har da jami’in lafiya, Jami’an tsabta, da kuma masu kula da abinci.

 

Mutane bakwai ne suka samu raunuka a hadarin, amma ba a rasa rai ba.

 

Minista Alkali ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin da lamarin ya faru, inda ya yaba da ƙoƙarin jami’an tsaro da ma’aikatan Hukumar Jirgin Ƙasa ta Ƙasa, wato NRC, wajen tabbatar da tsaron fasinjoji da kuma saurin mayar da hanyar ta koma aiki.

 

Ya ƙara da cewa ma’aikatan NRC na aiki dare da rana domin tabbatar da cewa ayyukan jirgin ƙasa sun dawo cikin ƙanƙanin lokaci.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid September 3, 2025 September 3, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Sojojin Isra’ila Sun Kasa Mamayar ko da ƙauye ɗaya a Lebanon — Hezbollah

Attajdid Attajdid November 12, 2024
Dokar ta Baci a jahar Jigawa kan fannin ilimi
Jigawa LG Election Holds Peacefully
Netanyahu Yana Tsoran Za a Kawo Masa Hari Daga Lebanon 
Gamnatin Nigeria tana kokarin kammala tsarin manufofin iyali na kasa
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?