Jaridun ƙasa da ƙasa sun ruwaito cewa dakarun Isra’ila sun kai hari ta sama kan wani wuri da ake zargin kakakin Hamas na ɓoye, duk da cewa har yanzu ba a tabbatar da ko an samu nasarar jikkata ko kashe shi ba.
Abu Obeida ya kasance ɗaya daga cikin fitattun muryoyin Hamas tun farkon rikicin, yana fitar da sakonni kan ci gaban yaƙin da kuma mayar da martani ga Isra’ila.
Tun bayan da yaƙin ya ƙara tsananta a Gaza, Isra’ila ta zage damtse wajen neman manyan jagororin Hamas da nufin raunana karfin ƙungiyar.
Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga Hamas ko Isra’ila da ke tabbatar da makomar Abu Obeida bayan wannan farmaki.
At’tajdid News.




