By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: KARNUKA YAN BINDIGA SUNYI KALACE DA JARIRAI A ZAMFARA
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > KARNUKA YAN BINDIGA SUNYI KALACE DA JARIRAI A ZAMFARA
News

KARNUKA YAN BINDIGA SUNYI KALACE DA JARIRAI A ZAMFARA

Attajdid
Last updated: 2025/05/14 at 5:09 PM
Attajdid Published May 14, 2025
Share
SHARE

KARNUKA YAN BINDIGA SUNYI KALACE DA JARIRAI A ZAMFARA

 

Ɗan Majalisa mai wakiltar yankin Kaura Namoda da Birnin Magaji a jihar Zamfara, Hon. Aminu Sani Jaji, ya bayyana yadda ’yan bindiga suka bai wa karnuka wasu jairirai tagwaye da aka haifa a daji su ci.

 

Jaji, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba.

 

Ya ce maharan sun sace wata mata mai ciki a wani ƙauye da ke Zamfara, kuma bayan ta haihu, ’yan bindigar suka jefa wa karnuka domin ci su.

 

Yadda ’yan bindiga suka kashe jarirai, suka bai wa karnuka namansu a Zamfara

Ɗan majalisar ya ce a yanzu Zamfara ta zama tarkon mutuwa a wajen jama’ar gari.

 

 

Jaji, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba.

 

Da muna kan mulki ni da Lamido da mun ƙalubalanci Tinubu — Amaechi

Zaɓen 1993: IBB ya wallafa ba daidai ba a littafinsa — Sule Lamiɗo

Ya ce maharan sun sace wata mata mai ciki a wani ƙauye da ke Zamfara, kuma bayan ta haihu, ’yan bindigar suka jefa wa karnuka domin ci su.

 

 

Ya kuma ruwaito yadda wani yaro mai fama da cutar farfaɗiya ya mutu bayan da ya faɗi a dajin.

 

 

Ya ce ’yan bindigar sun nemi mahaifin yaron da ya miƙa musu shi, gudun ka da ya rasa sauran yaransa ya umarci yaron ya je wajensu.

 

Yaron ya yarda ya tafi, kuma nan take suka harbe shi har lahira.

 

Ɗan majalisar ya ce irin waɗannan abubuwa na nuna cewa gwamnati ta kasa kare mutane a Zamfara.

 

 

Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta ɗauki matakin gaggawa.

 

 

Ya bayyana yadda ya yi alƙawari kafin zaɓen 2023, inda ya faɗa wa jama’a cewa sabuwar gwamnati za ta bai wa tsaro muhimmanci, amma yanzu al’amura sun ƙara lalacewa.

 

“Mun cuci mutanenmu. Ba sa iya zuwa gonakinsu. Tattalin arziƙinsu ya rushe. Mutane da dama sun rasa matsuguninsu, kuma babu wani taimako daga gwamnati,” in ji shi.

 

Ya ce ya gana da wasu shugabannin tsaro har da Ministan Tsaro, amma babu wani canji da aka samu.

 

“Zamfara tana cikin aminci. Yanzu kuwa, tana daga cikin wuraren da rikici ya fi ƙamari. Kundin tsarin mulki ya ce gwamnati na da alhakin kare rayuka da dukiyoyi, amma hakan ba ya faruwa a yanzu.”

 

Da aka tambaye shi game da bai wa jama’a dama su kare kansu, sai ya ce doka ta fi komai.

 

“Mu ’yan majalisa ne, ba ma’aikatan tsaro ba. Ba za ce mutane su ɗauki makami ba. Amma gaskiya ne, mutane suna ganin yadda aka bar su,” in ji Jaji.

 

Mai Rahoto

Mujahid Muhammad Tasiu

AT-TAJDID NEWS

 

 

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid May 14, 2025 May 14, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

International Fistula Day: Experts Call For Public Awareness on Family Planning

Attajdid Attajdid May 24, 2025
MAAIKATAN JINYA SUN JANYE YAJIN AIKIN YAU
Group Backs Tinubu and Namadi, 2nd Term Initiates Fundraising for Nomination Form
Borno: Zulum begins first North’s rail network
MIJI DA MATA DA ‘YA’YANSU SUN RASU SAKAMAKON CIN CIN ABINCI MAI GUDA A JAHAR SOKOTO.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?