Gwamnatin Jihar Sokoto ta raba tallafi ga iyalan da hatsarin jirgin ruwa ya rutsa da su a garin Rinaye, karamar hukumar Shagari.
Hadarin,ya yi sanadiyyar mutuwar mutane bakwai ciki har da mata uku da yara hudu.
Tawagar da gwamna Ahmad Aliyu ya tura ta raba tallafin kuɗi na Naira miliyan huɗu ga iyalan da abin ya shafa, tare da kayan abinci irin su shinkafa, gero da dawa.
Gwamna Aliyu, wanda ya yi jawabi daga ƙasar Saudiyya inda yake aikin Umara, ya nuna alhinin sa game da wannan iftila’in tare da tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta samar da jiragen ruwa masu amfani da injin da rigar shiga ruwa domin rage haɗarin jiragen ruwa a jihar.
Wannan matakin na cikin shirin gwamnati na kashe sama da naira miliyan dubu 1 domin ƙarfafa shirin kare jama’a daga haduran kwale kwale musamman a yankunan da ke da ambaliyar ruwa ta fi shafa.




