Gwamnatin Jihar Jigawa ta dauki nauyin dalibai 184 domin karo karatun likitanci a kasashen waje.
Wannan na daga cikin kokarin gwamnatin jihar na rage ƙarancin likitoci a jihar.
Daga cikin daliban, 160 an tura su jami’ar Near East University dake Cyprus, yayin da sauran aka turasu jami’ar Integral University dake kasar India.
Gwamnatin ta ce wannan shiri na da nufin samar da karin kwararrun likitoci a Jigawa, musamman ma wajen karfafa wa mata gwiwa su shiga harkar likitanci.
Rahotanni sun nuna cewa gwamnati ta kashe sama da Naira miliyan dubu 4 domin biyawa daliban kudin makaranta, da masauki,da abinci,da kudin jirgi da sauran bukatun daliban.
Wasu daga cikin daliban da suka dawo gida hutu sun nuna godiyarsu ga gwamnatin.
A cikin yarjejeniyar da aka sanya hannu, daliban za su dawo su yi aiki a Jigawa na tsawon shekaru daidai da lokacin da suka dauka suna karatu a kasashen waje.
Baya ga daliban likitanci, akwai kusan dalibai 15 da ba na likitanci ba, ciki har da wadanda aka kwaso daga kasar Sudan lokacin rikici, wadanda suma suke amfana daga shirin.




