By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Turkiyya ta yi tur da harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a Qatar
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Turkiyya ta yi tur da harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a Qatar
News

Turkiyya ta yi tur da harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a Qatar

Attajdid
Last updated: 2025/09/13 at 6:04 PM
Attajdid Published September 13, 2025
Share
SHARE

Turkiyya ta yi tur da harin da Isra’ila ta kai kan tawagar Hamas a Qatar

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta yi kakkausan gargaɗi da yin tur da “manufofin Isra’ila na faɗaɗa mamaya.”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar da wata sanarwa mai lamba: 183, a ranar 9 ga Satumban 2025, “Dangane da Harin Isra’ila kan Doha, Babban Birnin Qatar”.

 

“Muna Allah wadai da harin da Isra’ila ta kai kan tawagar tattaunawar Hamas a Doha, babban birnin Qatar,” sanarwar ta fara da cewa.

 

Ma’aikatar ta nuna cewa ayyukan Isra’ila suna da rikitarwa; a gefe guda tana nuna kamar tana son tattaunawa don kawo karshen yakin Gaza da dawo da mutanen Isra’ila da aka yi garkuwa da su, amma a gefe guda tana ƙara tayar da tarzoma har ma a wasu yankunan da ba na Falasdinu.

 

“Kai hari kan tawagar tattaunawar Hamas yayin da ake ci gaba da tattaunawar tsagaita wuta yana nuna cewa Isra’ila tana son ci gaba da yaƙi, ba zaman lafiya take nema ba.”

Ma’aikatar ta ce Isra’ila tana ƙara samun sabbin abokan gaba ta hanyar kai hare-hare ba tare da wani dalili ba: “Da wannan hari, Qatar, wadda ta shiga tsakani wajen tattaunawar tsagaita wuta, ta shiga jerin kasashen da Isra’ila ke kai wa hari a yankin.”

 

“Wannan hujja ce a fili kan manufofin fadada yankin da Isra’ila ke yi da kuma daukar ta’addanci a matsayin manufofin gwamnatinta.”

 

Ma’aikatar ta sake jaddada goyon bayanta ga Qatar wadda ta kasance mai shiga tsakani a yaƙin Gaza, tana daukar nauyin tattaunawa don kawo karshen wahalhalun da al’ummar Falasdinu ke sha.

 

“Muna tare da Qatar kan wannan mummunan hari da ya nufi keta ikon mallaka da tsaronta. Muna sake kira ga al’ummar duniya da su matsa wa Isra’ila lamba don kawo karshen hare-haren da take ci gaba da kaiwa a Falasdinu da yankin.”

 

Mai rahoto

Mustapha Garba Usman

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid September 13, 2025 September 13, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

Jigawa APC, NNPP Holds Primary Election For Garki/Babura By-election

Attajdid Attajdid July 19, 2025
Biden Adviser Sullivan Holds ‘rare’ Talks With Top Chinese Army Official.
Gwamnatin Kano ta haramta bikin ‘ƙauyawa day’ da soke lasisin gidajen bukukuwa
Dakarun Qassam Sun Kwace wata Mota Dauke Da Jirgi mara Matuki Yayin Da Isra’ila take Lugudan Wuta a Lebanon
Kotu Ta Dage Ci Gaba Da Sauraren Shaidu A Shari’ar Da Ake Zargin Matashin Da Ya Cinnawa Masallata Wuta A Kano
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?