Wani mutum mai shekara 50, mai suna Modu Isa, mazaunin unguwar Hausari a garin Bama, Jihar Borno, ya tsira daga yunƙurin kashe kansa bayan ya daba wa cikinsa wuka sau uku sannan ya yanke al’aurarsa saboda rikicin aure.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne bayan tsohuwar matarsa ta ƙi amincewa ta dawo gidansa, duk da roƙonsa da ƙoƙarin da ya yi na shawo kanta. Wannan ya jefa shi cikin tsananin bakin ciki da damuwa har ya kai ga ɗaukar matakin mummunan yunƙurin kashe kansa.
Shaidu daga unguwar sun ce an garzaya da shi asibiti bayan faruwar lamarin, inda likitoci suka yi masa aikin gaggawa domin ceton rayuwarsa. An ce yanzu haka yana samun kulawa ta musamman a asibitin gwamnati na Bama.
Hukumomi da mazauna yankin sun bayyana damuwa kan wannan abin tashin hankali, tare da jan hankalin jama’a da su guji ɗaukar irin waɗannan matakan illa a lokacin damuwar aure ko wata matsala ta rayuwa.




