Isra’ila ta kashe mutane 48 a arewacin Gaza
Hare-haren sama da Isra’ila ta kai arewacin Gaza da tsakar dare sun kashe Falasɗinawa aƙalla 48.
Wani asibitin Indonesia a yankin ya ce daga cikin waɗanda aka kashen akwai ƙananan yara 22 da kuma mata 15, a garin Jabalia da kuma wasu sansanonin ƴab gudun hijira.
Wani bidiyon da aka yaɗa ya nuna gomman gawawwaki a ƙasa.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce tana nazari a kan rahoton hare-haren nata.
Dama dai ta gargaɗi mutanen da ke zaune a Jabalia da ƙauyukan da ke kusa da shi, su fice kafin ranar Talata bayan wata wata ƙungiyar Falasɗinawa ta ƙaddamar da harin roka a kan Isra’ila.
Wannan na zuwa ne yayin da hukumar bayar da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ta nemi kwamitin tsaro na majalisar ya ɗauki matakin kawo ƙarshen kisan gilla a Gaza.
BBC Hausa
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu
AT-TAJDID NEWS




