By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4
NewsUncategorized

Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4

Attajdid
Last updated: 2025/08/06 at 1:06 PM
Attajdid Published August 6, 2025
Share
SHARE

Yadda ’yan bindiga suka sace Zamfarawa 150 a cikin kwana 4

’Yan bindiga sun sace mutum 150 a mabanbantan hare-haren da suka kai kauyuka daban-daban na jihar Zamfara a cikin kwana hudu.

’Yan bindiga sun sace mutum 150 a mabanbantan hare-haren da suka kai kauyuka daban-daban na jihar Zamfara a cikin kwana hudu.

 

Kakakin Gwamnatin jihar ta Zamfara, Mahmud Mohammed Dantawasa ne ya tabbatar da hakan ga BBC.

 

Sai dai duk da yake bai bayyana hakikanin adadin mutanen da aka sace ba, amma ya ce gwamnatinsu na iya kokarinta wajen ganin ta ceto su.

Haka na zuwa ne a daidai lokacin da malamin addinin Musuluncin nan mazaunin Kaduna, Sheikh Musa Yusuf Asadus-Sunna, ya ce kwamitin zaman lafiyar da yake jagoranta ya sami nasarar kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin kasurgumin dan bindigar nan, Bello Turji, da Gwamnatin Tarayya.

 

Tuni dai yarjejeniyar ta kai ga sakin mutum 32 da aka yi garkuwa da su da kuma mika wasu tarin makamai ga gwamnati.

 

Mazauna yankunan sun ce ’yan bidnigar da ke dauke da muggan makamai ne a tsawon kwanakin suka kai hari kauyukan Sabon Garin Damri da Dakko Butsa (wanda ke da iyaka da jihar Sakkwato), da Tungar Abdu Dogo da Tungar Sarkin Daji da Sadeda da kuma kauyen Tungar Labi.

Mutanen sun ce galibi ’yan bindigar sun fi kaddamar da hare-haren ne cikin dare lokacin da mutane suke bacci, ko kuma lokacin da ake yin ruwan sama.

 

Kazalika, wasu majiyoyin kuma sun ce lalacewar hanyoyin jihar na taka muhimmiyar rawa wajen kara ta’azzarar hare-haren, saboda jami’an tsaro kan sha bakar wuya kafin su iya shiga yankunan su kai wa jama’a dauki cikin gaggawa.

 

Mai rahoto

Mustapha Garba Usman

You Might Also Like

Speakers Forum Congratulates Kwara, Katsina Speakers for Securing Governorship, Senate Tickets

Jigawa Governor: Our One Million Votes for Tinubu Are Non-Negotiable , Irreversible

Governor Namadi Affirmed as APC Jigawa State Gubernatorial Candidate for 2027

APC Primaries: Jigawa Speaker Retains Ticket Unopposed

Nursing Mother Inmate Freed as Jigawa NLC Women’s Wing Clears Her Court Fines

Attajdid August 6, 2025 August 6, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
News

INTERNATIONAL DAY OF MENSTRUAL HYGIENE: “Exposing an age old stigma deeply rooted in our traditions”.  

Attajdid Attajdid June 1, 2025
Hamas ta sanar da kashe sojojin Isra’ila da dama da jikkata wasu
Reps Investigate 2024 Hajj
SHIRIN SABON MAMAYA A GAZA: HANA ZAMA, KORA, DA ƘARA IYAKA
An Soke Tafiyar Shettima Zuwa Samoa Bayan Gilas ɗin Jirginsa ya Lalace a Amurka
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?