Wata sabuwa,
Rahoto daga tashar Channel 12 ta Isra’ila ya bayyana cewa rundunar sojin Isra’ila na shirin kaddamar da cikakken mamaya a birnin Gaza City, tare da shirin korar fiye da mutane 900,000 daga yankin.
Ana sa ran wannan mamaya za ta biyo bayan wasu makonni na shirye-shiryen dabarun tsaro da tsarin kai daukin gaggawa ga mutanen da za su rasa matsuguni.
Rahoton ya kuma ce ana ci gaba da tattaunawa a cikin kwamitin tsaron Isra’ila kan yiwuwar ƙara yankin da aka ware a matsayin buffer zone zuwa cikin yankin da Isra’ila ke iko da shi.
Ana hasashen za a kashe kimanin shekel biliyan ɗaya (shekara biliyan ɗaya na Isra’ila) wajen kafa sabbin cibiyoyin raba agaji ga waɗanda rikicin ya shafa.
Binciken ya kara da cewa ana sa ran Amurka za ta bayar da tallafin jin ƙai ga wannan sabon mataki, wanda kungiyoyi masu rajin kare hakkin bil’adama ke kalubalantar da cewa yana kara tsananta halin da al’umma ke ciki.
M.B.S. Gama
At-tajdid News




