Gwamnatin tarayya ta ce ta kudiri aniyar aiwatar da sauye-sauye da za su kyautata walwala da kwarewar ma’aikatan Jinya a fadin kasar nan tun bayan da Kungiyar ma’aikatan Jinya da Unguwar zoma ta kasa ta Janye yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai da ta fara a karshen makon da ya gabata.
Yajin aikin dai ya haifar da tsaiko ga harkokin kiwon lafiya a fadin kasar nan a saboda yadda Ma’aikatan lafiya da Unguwar zoma duk su ka dakatar da aiyukansu a saboda rashin cimma daidaito akan kyautata walwalarsu da amincewa da kwarewarsu da kuma sake fasalin sharuddan aiyukansu.
Daga bisani ne dai aka cimma fahintar juna a tsakanin Gwamnatin tarayya da kuma Kungiyar ma’aikatan Jinya da Unguwar Zoma ta kasa bayan da Ministan kwadago da samar da aiyukan yi na kasa Muhammad Maigari Dingyadi ya shiga tsakani har aka cimma daidaito akan wasu abubuwa guda Bakwai tare da Janye yajin aikin gargadin a ranar Juma’a 1 ga watan Augustan shekarar 2025.
A cewar rahotanni daga cikin muhimman abubuwa guda Bakwai da aka cimma fahintar juna akai akwai tabbaci da gwamnatin tarayya ta bayar na kyautata aiyukan ma’aikatan jinya a fadin kasar nan wanda majalisar aiyuka ta kasa ta amince da shi tun a shekarar 2016.
Hakanan ma’aikatar lafiya da lura da Walwalar al’umma ta kasa za ta hada hannu da Ofishin shugaban ma’aikata na Tarayya wajen ganin an aiwatar da tsarin.
Mai Rahoto
Nura Abubakar Musa




