Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III, ya zargi malaman addini da yaudarar mabiyansu domin samun abin duniya.
Sarkin Musulmi, wanda kuma shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), ya gargaɗe su a kan hakan sannan ya umarce su da su tuba, su riƙa gudunar da wa’azi ta hanyar ingantacciyar koyarwar Musulunci don gina al’umma ta gari.
Ya bayyana haka ne a wajen taron yankin kan rikicin da ke haifar da sauyin yanayi a Arewacin Najeriya, wanda aka gudanar ranar Litinin a Kaduna.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa, ofishin kula da addinai na Jihar Kaduna tare da haɗin gwiwar International Alert ne suka shirya taron.
Mai Rahoto
Mujahid Muhammad Tasiu




