Yaƙi tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF ya mayar da birane maƙabartu, sannan ya sa ana barin gawawwaki a yashe ba tare da an binne su ba. Garuruwa da dama sun zama kufai.
Kimanin 30% na ‘yan Sudan sun gudu daga gidajensu.
Ƙungiyoyin agaji sun yi gargaɗin cewa ainihin adadin waɗanda suka mutu zai iya haura abin da ake bayar da rahoto — ba a iya shiga wurare da dama, sannan rashin hanyoyin sadarwa ya ɓoye ainihin ta’annatin da ake yi.
Rashin imanin da ake yi a zahiri yake, amma mai yiwuwa abin da muka sani bai taka kara ya karya ba. TRT African hausa.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




