Yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta shiga kwana na uku bayan yaƙin kisan ƙare-dangin da Isra’ila take yi a yankin da ya kashe Falasɗinawa fiye da 47,035, ciki har da wani yaro da ta kashe a Rafah da kuma sace gomman mutane a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.
Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana shakkunsa game da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza a yayin da aka tambaye shi kan ko yana da ƙwarin gwiwa game da yiwuwar aiwatar da dukka matakai uku na yarjejeniyar.
A yayin da yake jawabi ga manema labarai a ofishin shugaban ƙasa bayan sanya hannu kan dokokin shugaban ƙasa, Trump ya ce yankin Gaza da aka yi wa ƙawanya ya yi kama da “wani babban wuri da aka rusa” kuma ya kamata a sake gina shi a wani tsari na daban.
Shugaban Amurka Donald Trump ya soke takunkuman da tsohuwar gwamnatin Biden ta ƙaƙaba wa Isra’ilawa ‘yan kama-wuri-zauna bisa musguna wa Falasɗinawa a Gaɓar Yammacin Kogin Jordan, kamar yadda sabon shafin intanet na Fadar White House ya bayyana.
Shafin ya ce Trump ya soke Dokar Shugaban Ƙasa mai lamba 14115 wadda aka amince da ita ranar 1 ga watan Fabrairun 2024, wacce kuma ta amince a sanya takunkumai kan “mutanen da ke yin tarnaƙi game da zaman lafiya da tsaron Gaɓar Yammacin Kogin Jordan.” TRT African Hausa.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




