Firayim Ministan Spain, Pedro Sánchez, ya bayyana cewa ƙasarsa ba za ta ci gaba da hulɗa da Isra’ila ba saboda yadda take ci gaba da kisan al’ummar Falasdinu a Gaza.
A gaban majalisar dokoki a Madrid, Sánchez ya ce:
“Ba mu yin kasuwanci da kasa mai aikata kisan kiyashi. Mun ɗauki matsaya. Spain ta bar wannan hulɗa.”
Wannan kalami mai ƙarfi ya jawo ce-ce-ku-ce a duniya, inda Isra’ila ta kira jakadan Spain domin nuna fushinta.
Spain na daga cikin ƙasashen Turai da suka amince da kafa ƙasar Falasdinu a hukumance, kuma a baya sun soke yarjejeniyar saye da Isra’ila dangane da makamai.
A taƙaice, Sánchez ya bayyana cewa Spain ba za ta zama ɓangare na zalunci da cin zarafi ba.
Shin ko yaushe sauran ƙasashen duniya za su farka su dauki irin wannan matakin??
#Palestine #Spain #PedroSanchez #FreePalestine #Gaza #Diplomacy #Justice
Muazzam Hamza




