An samu jafa kuri’ar jin ra’ayin jama’a na Jami’ar Harvard da Harris Foundation mutane kashi 21% na masu jefa kuri’a Amurka sun goyi bayan Hamas da kashi 87% ‘yan jam’iyar Democrats da 81% ‘yan jam’iyar Republican wadanda suka goyi bayan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza kashi 57% na Amurkawa masu jefa kuri’a sun tabbatar da cewa Hamas ta amince da yarjejeniyar saboda Trump, sannan kuma kashi 43% sun danganta hakan da Biden.
Kafar yada labaran Isra’ila ta kawo yadda Jami’an Isra’ila sukayi matukar kaduwa a lokacin da suka ga yadda aka sako wadanda aka yi garkuwa da su a cikin jama’a a gaban mayakan Hamas a tsakiyar Gaza. Jami’an Isra’ila za su sanar da masu shiga tsakani cewa wurin da aka sako mutanen kamar yadda aka yi ba a yarda da shi ba.
Jaridun yahudawan sun yi sharhi kan al’amuran siyasar makomar Netanyahu bayan kawo karshen yakin Gaza, da suka hada da shari’ar da aka yi masa kan laifukan cin hanci da rashawa, da wargajewar gwamnatin hadin gwiwa, da kuma gagarumin koma baya.
Jagoran ‘yan adawar Isra’ila Yair Lapid ya bayyana cewa “Yakin ya kare kuma yana da kyau a kawo karshensa, kuma dole ne a aiwatar da yarjejeniyar da masu garkuwa da mutane suka yi gaba daya.”
Ben Gvir ya ce “Matakin tarihi na Trump na dage takunkumin da gwamnatin Biden ta kakaba wa mazauna Yammacin Kogin Jordan kuma gyara ne ga zaluncin da ya dau shekaru ana aiwatarda shia yankin”
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.





