Ɗaya daga cikin manyan jagororin Hamas da ba sa zama a cikin Gaza, Khali al-Hayya, da sauran waɗanda suke shige wa ƙungiyar gaba a tattaunawa da sauran al’amuran shugabanci sun bar birnin Doha, kamar yadda gwamnatin Qatar da wani babban jami’in gwamnatin Falasɗinu suka bayyana.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Qatar ya ce yanzu ofishin Hamas ba ya wani aiki sosai saboda Qatar ta dakatar da yunƙurin da take yi na shiga tsakani domin samar da maslahar tsagaita wuta a Gaza, duk da cewa ta ce ba wai ta rufe ofishin ba ne baki ɗaya.
Jami’in gwamnatin Falasɗinun ya shaida cewa jagororin na Hamas sun canja salonsu a yankin, kuma za su daina bayyana inda suke domin kiyaye mutuncin ƙasashen da suke zaune.
Amma sun ce akwai alamu Hayya na Turkiyya domin ya sha yin tafiya zuwa ƙasar a cikin watanni biyu da suka gabata.
Jami’in ya ƙara da ewa Qatar ba ta kori ‘yan Hamas ba, amma dai ya ce ƙasar na taka-tsantsan ne domin gudun shiga matsala da gwamnatin Amurka. BBC Hausa.
Mai rahoto;
Ibrahim Usman Adam.
At-tajdid News.




