Firaministan ya isa Nijeriya a ranar Asabar, inda yasamu kyakykyawar tarba daga tawaga ta musamman ta Shugaba Bola Tinubu karkashin jagorancin ministan Abuja Nyesom wike.
An gudanar da kwarya- kwaryan fareti ga mista Modi a Fadar Shugaban Nijeriya kafin fara tattaunawa tsakanin su.
Wannan ne karo na farko da firaminista daga Indiya zai je Nijeriya tun bayan zuwan da Manmohan Singh ya yi zuwa ƙasar a shekarar 2007.
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu da Firaministan lndiya Narendra Modi sun tattauna kan batun hadin gwiwa ta bangaren yaki da ta’addanci da tsaron cikin teku gami da sanar da juna bayanan sirri a jiya Lahadi 17 ga watan nuwamba.
Shugabannin biyu sun samu nasarar ganawa da juna ne a Fadar Shugaban Nijeriya dake Abuja, kamar yadda mai magana da yawun Shugaban Bayo onanuga yabayyana awata sanarwa da ya fitar.
A daidai lokacin da ake samun barazana a mashigar tekun Gunea da tekun Indiya, inda suka tattauna kan batun tsaro da kuma yaki da ‘yan fashin teku.
Modi ya yiwa Nigeria alkawarin tai makawa Nigeria ta bangaren tsaro, inda ya bayyana cewa Indiya kasace amin tacciya wajen samar da kayayyakin tsaro.
An kammala tattaunawar da saka hannu kan batun yar jejeniya da kuma shirye shoryen na al ‘adu gamida habbaka dan gan takar kasashen ta bangarori da dama.
Daga bisani Shugaban Nijeriya ya karrama mista Modi da lambar yabo ta GCON. Ƙarshen
Mai Rahoto;
Zainab SulaimanNaibawa.
At-tajdid News.




