Isra’ila ta Kai Munanan Hare-hare a Gazza ya yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 153 a Cikin Awa 24.
Adadin wadanda suka mutu sakamakon harin da Isra’ila ta kai a Gaza ya haura 153 a cikin sa’o’i 24 kacal, a cewar ma’aikatar lafiya ta Gaza. Isra’ila na shirin kai wani gagarumin farmaki a yankin Falasɗinawa da ta yi wa ƙawanya, inda aka kashe fiye da mutum 53,000, galibi mata da yara tun daga watan Oktoban 2023.
Fiye da mutane 300 ne aka kashe tun daga ranar alhamis ɗin da ta gabata, ciki har da waɗanda ke zaune a wuraren da ake kira “yankuna masu aminci,” in ji jami’an kiwon lafiya na Falasdinu, wanda hakan ya kasance mafi muni a yakin tun bayan kawo ƙarshen tattaunawar tsagaita bude wuta a watan Maris na 2025.
A wani rahotan da At-tajdid News ta samu daga yankin gabas ta tsakiya ya bayyana Isra’ila ta ƙaddamar da wani sabon farmaki ta ƙasa a arewaci da kudancin Gaza inda ta yi masa laƙabi da “Operation Gideon’s Chariots”.
Wannan na zuwa ne bayan Isra’ilar ta kashe fiye da mutum 153 a cikin kwana guda.
Mai rahoto;
M.B.S.Gama.
At-tajdid News.




