By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu Rasha a ranar Litinin
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu Rasha a ranar Litinin
News

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu Rasha a ranar Litinin

Attajdid
Last updated: 2025/05/25 at 3:18 PM
Attajdid Published May 25, 2025
Share
SHARE

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Fidan zai kai ziyarar aiki ta kwana biyu Rasha a ranar Litinin

 

Ana sa ran wannan ziyarar za ta ƙara yauƙaƙa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu a muhimman ɓangarori waɗanda suka haɗa da kasuwanci da makamashi da yawon buɗe ido.

 

 

Ministan Harkokin Wajen Turkiyya, Hakan Fidan, zai kai ziyara zuwa Tarayyar Rasha a ranakun 26 zuwa 27 ga Mayu, 2025, bisa gayyatar gayyatara da takwaransa Sergey Lavrov ya yi masa a hukumance.

 

A lokacin wannan ziyara, ana sa ran Fidan zai gana da Shugaban Rasha, Vladimir Putin, tare da gudanar da tattaunawa a hukumance da Lavrov a birnin Moscow, kamar yadda majiyoyin Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya suka bayyana a ranar Asabar.

 

Ziyarar za ta mayar da hankali kan muhimman fannoni na dangantakar Turkiyya da Rasha, inda ake sa ran Fidan zai yi cikakken nazari kan haɗin gwiwar kasashen biyu a fannonin kasuwanci, makamashi, da yawon shakatawa.

 

Haka kuma, za a tattauna matakan da za a ɗauka don yauƙaƙa dangantakar ƙasashen biyu.

 

Baya ga ganawarsa da Lavrov da Putin, Fidan zai kuma tattaunawa da wasu manyan jami’an gwamnatin Rasha.

 

Jami’an haɗa da Mataimakin Shugaban Ma’aikatar Shugaban Kasa, Vladimir Medinsky, wanda ya jagoranci tawagar Rasha a tattaunawar Rasha da Ukraine da aka gudanar a Istanbul a ranar 16 ga Mayu, da kuma Ministan Tsaro, Andrei Belousov, da wasu manyan jami’ai.

 

Tattaunawar za ta kuma ƙunshi batutuwan da suka shafi ƙarin haɗin kai tsakanin ƙasashen biyu.

 

Ana sa ran a yayin tattaunawar Fidan zai ƙara jaddada ƙoƙarin da Turkiyya ke yi wajen samar da zaman lafiya mai ɗorewa da adalci a rikicin da ke tsakanin Rasha da Ukraine, tare da bayyana jin daɗinsa kan ci gaban da aka samu kwanan nan da zai iya taimakawa wajen samun nasara a wannan fanni.

 

Haka kuma, Fidan zai sake jaddada shirye-shiryen Turkiyya na ci gaba da taka rawa a matsayin mai shiga tsakani a tattaunawar gaba tsakanin ɓangarorin da ke rikici, kamar yadda ta yi a baya a shekarar 2022 da kuma a zagayen tattaunawar da aka yi a ranar 16 ga Mayu.

 

Ziyarar za ta kuma ƙunshi musayar ra’ayoyi kan batutuwan yankin da na kasa da kasa, ciki har da halin da ake ciki a Syria, Gaza, da yankin Kudancin Caucasus

 

Ziyarar da Fidan ya kai ta ƙarshe Rasha ya yi ta ne tsakanin 10 zuwa 11 ga Yunin, 2024, inda ya halarci taron BRICS+, sannan daga baya ya halarci taron Ƙolin BRICS a ranar 24 ga Oktobar 2024, tare da Shugaba Recep Tayyip Erdoğan.

 

Ganawa ta baya-bayan nan da Fidan da Lavrov suka yi sun yi ta ne a ranar 12 ga Afrilun 2025, a gefen taron Antalya Diplomacy Forum. Kafin wannan, Lavrov ya ziyarci Turkiyya a ranar 23 ga Fabrairun 2025, domin tattaunawar bangarorin biyu.

 

Haka kuma, ya halarci taron dandalin hadin kai na yankin 3+3 da Fidan ya shirya a Istanbul a ranar 18 ga Oktobar 2024. Bugu da kari, ministocin biyu sun yi ganawa ta ɓangarorin biyu a lokacin taron ministocin harkokin waje na G20 da aka gudanar a Johannesburg a ranar 20 ga Fabrairun 2025.

 

Mai Rahoto

Mujahid Muhammad Tasiu

AT-TAJDID NEWS

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid May 25, 2025 May 25, 2025
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News

An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja

Attajdid Attajdid May 25, 2025
Nigeria/Israel Security Pact
100 Days Community Association Commends LG Boss For Purposeful Leadership 
Protest Continue at 4 LGs Despite 24 Curfew In Jigawa State.
AN KAI HARI  YANKIN TILLABERI NA JAMHURIYAR NIJAR DA YAKE IYAKA DA MALI DA BURKINA FASO.
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?