Harin ‘Yan Ta’adda Ya Kashe Sojojin Hadin Gwiwa Biyar a Arewa Maso Gabashin Najeriya
A safiyar ranar Juma’a, 16 ga Mayu, 2025, ‘yan ta’adda daga kungiyar Islamic State West Africa Province (ISWAP) sun kai hari kan sansanin dakarun hadin gwiwa na Multinational Joint Task Force (MNJTF) da ke garin Wulgo, kusa da iyakar Najeriya da Kamaru. Harin ya yi sanadin mutuwar sojoji biyar, hudu daga Najeriya da ɗaya daga Kamaru.
Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan ta’addan sun kona motocin yaki masu kariya guda biyu da manyan motocin soja guda biyar, sannan suka kwace babura daga masu farauta na yankin da ke taimakawa sojoji wajen yaki da ‘yan ta’adda.
Wannan hari na zuwa ne bayan wani hari makamancin haka da aka kai a watan Maris a sansanin soja na Rann, inda aka kashe sojoji hudu kuma aka sace wasu.
A cikin watanni biyu da suka gabata, an kai hare-hare kan sansanonin soja fiye da goma a yankin arewa maso gabashin Najeriya, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da 100, ciki har da fararen hula.
Shugaban hafsoshin tsaro na Najeriya, Janar Christopher Musa, ya bayyana cewa an dauki matakan gaggawa don dakile hare-haren ‘yan ta’adda, tare da alkawarin samar da karin kayan aiki ga dakarun da ke fuskantar ‘yan ta’adda a yankin.
Hare-haren da ‘yan ta’adda ke kaiwa a yankin sun kara tsananta matsin lamba ga dakarun Najeriya da na kasashen makwabta, yayin da kungiyar ISWAP da Boko Haram ke kara karfi da samun sabbin dabarun yaki.
Mai Rahoto
Hamza Muhammad sharif




