Ministan Babban Birnin Tarayyar Nijeriya Abuja, Nyesom Wike ya gargaɗi mabarata da ke kara-kaina a kan titunan birnin da cewa ko dai su daina ko kuma hukumomi su fara kama su a lokacin da talakan kasar yake cikin matsanincin yunwa ta yadda bai iya cikin abinci sau uku a rana da kuma talauci da ya yi kaka-gida a kasar.
Wike ya fadi hakan ne a ranar Talata yayin ƙaddamar da fara gina wani titi a unguwar Katampe da ke birnin.
Ya koka cewa yawan mabarata a titunan Abujan lamari ne da ke da barazana ga tsaron mazauna birnin.
Daga nan sai ya ba da sanarwar cewa daga ranar Litinin mai zuwa, 27 ga watan Oktoban 2024 za a fara kama duk wanda aka gani yana bari a titi.
At-tajdid News.




