Rundunar sojin Isra’ila ta kai sabbin hare-hare ta sama a Beirut, inda ta fi mayar da hankali a yankunan da ke kudancin wajen babban birnin na Lebanon, bayan Isra’ila ta yi barazanar kai harin bama-bamai kan gine-gine cibiyar harkokin kudi ta Qard al Hassan da ke da alaka da Hezbollah.
Jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare tara cikin awa daya a kan rassan cibiyar da ke Hayy al Sellum, Borj al Barajneh, da kuma Ghobeiry a kudancin Beirut,a cewar kamfanin dillancin labaran Lebanon na National News Agency.
Tun da farko, rundunar sojin Isra’ila ta yi barazanar kai hari a “muhimmiyar cibiyar harkokin kudi” ta Hezbollah a Lebanon.
Qard al Hassan na daya daga cibiyoyin kudi na Hezbollah, wadda aka kafa a shekarun 1980 domin bayar da sadaka ga al’umma.
An kunna jiniyar da ke nuna shiga haɗari mataki na 3, wanda ke nufin matsanancin haɗari a cikin sansanin sojojin tabbatar da zaman lafiya na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNIFIL) a garin Maarakeh, gundumar Tyre a kudancin Lebanon.
A cewar kamfanin dillancin labarai na Lebanon, an yi gargaɗin ne yayin da barazana take da girma a yankin, yayin da ake ci gaba da artabu da faɗan kan iyaka tsakanin sojojin Isra’ila da ƙungiyoyin yankin.
Jami’an UNIFIL da mazauna yankin sun shiga cikin barazana babba yayin da yanayin tsaro a kudancin Lebanon yake ci gaba da taɓarɓarewa.
Isra’ila ta yi iƙirarin cewa sojojinta na sama sun kai farmaki kan hedikwatar leƙen asiri ta Hezbollah, da kuma garejin aiki na ƙarƙashin ƙasa inda suke ƙera makamai a Beirut.
At-tajdid News.




