Ya sayi fam na takarar Kansila jiya ƴan bindiga sun bindigeshi a hanyar komawa gida a Zamfara
Daga: Zaharaddeen Zarumee Gusau.
Wani matashi da ya sayi fam na neman tsayawa takarar Kansila a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar PDP a jihar Zamfara, ya gamu da ajalinsa a hanyarsa ta komawa gida a jiya.
Labarin mutuwar ɗan takarar da ba a bayyana sunansa ba wanda ya karaɗe shafukan sada zumunta, ya bayyana cewa ya sayi fam ɗin ne domin neman takarar Kansila a mazaɓar Wuya ta ƙaramar hukumar Anka da ke jihar Zamfara.
Matashin ya gamu da ajalinsa ne kan hanyar komawa gida tsakanin Mayanci zuwa Anka, bayan da ƴan bindigar ɗauke da makamai suka tare motarsu suka yi garkuwa da mutanen da ke ciki, shi kuma suka bindige shi.
An dai yi gaggawar zuwa assibiti domin ceto ransa, amma sai dai rai ya yi halinsa.
A baya-bayan nan dai jihar Zamfara na fama da matsanancin hare-haren ƴan bindiga musamman a kan hanyar Gusau zuwa Funtuwa, to sai dai mahukunta suna cewa suna bakin ƙoƙarin su domin kawar da ƴan bindigar.
At’tajdid news




