By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
At'tajdid NewsAt'tajdid NewsAt'tajdid News
Notification Show More
Font ResizerAa
  • News
    • International News
  • Video
  • Lecture Audio
    • Tafsir
  • More
    • Books & Journal
      • Feature/Articles
    • Contact
    • Search Page
    • Blog
    • About Us
Reading: Rundunar ‘Yan Sandan Nigeria Ta Janye Jami’anta Daga Hedikwatar Kananan Hukumomin a Jahar Rivers
Share
Font ResizerAa
At'tajdid NewsAt'tajdid News
  • HomeHome
  • My Feed
  • My Interests
  • My Saves
  • History
  • Blog
Search
  • Quick Access
    • Home
    • Contact Us
    • About Us
  • Categories
    • News
    • International News
    • Video
    • Books & Journal
    • Feature/Articles
    • Lecture Audio
    • Tafsir
Have an existing account? Sign In
Follow US
At'tajdid News > Blog > News > Rundunar ‘Yan Sandan Nigeria Ta Janye Jami’anta Daga Hedikwatar Kananan Hukumomin a Jahar Rivers
News

Rundunar ‘Yan Sandan Nigeria Ta Janye Jami’anta Daga Hedikwatar Kananan Hukumomin a Jahar Rivers

Attajdid
Last updated: 2024/10/08 at 6:50 AM
Attajdid Published October 8, 2024
Share
SHARE

Rundunar ‘yan sandar jihar Rivers ta janye jami’anta daga dukkan sakatariyar ƙananan hukumomi 23 da ke jihar, hakan na zuwa ne bayan kammala zaɓen ƙananan hukumomin tare da rantsar da wadanda suka yi nasara.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Rundunar ‘yansandar, Grace Iringe-Koko , ta fitar da safiyar yau Litinin ta tabbatar da hakan.

Ta ce kwamishinan ‘yansanda na jihar ya bayar da umarnin ne ƙarƙashin umarnin Sifeto Janar, Kayode Egbetokun, wanda ya umarci a janye jami’an da ke samar da tsaro a dukkan hedikwatar ƙananan hukumomin jihar nan take.

Jam’iyar APP ce ta samu nasarar lashe zaɓen ƙananan hukumomi 22 a cikin 23, yayin da jam’iyar AA ta samu nasarar lashe zaɓen ƙaramar hukumar, Etche.

Jami’an ‘yansandan dai sun ƙarɓe iko da hedikwatar ƙananan hukumomin jihar Rivers a watan Yuni sakamakon rashin fahimta da ta shiga tsakanin Kantomomi masu goyon bayan gwamnan jihar mai ci Siminalayi Fubara da kuma tsoffin shugabannin ƙananan hukumomi na gwamnatin da ta gabata da ke goyon bayan tsohon gwamnan jihar kuma ministan Abuja, Nyesom Wike.

Gwamna Siminalayi Fubara na takun saƙa da tsohon uban gidansa, ministan Abuja, Nyesom Wike, inda kowanensu ke son samun rinjaye a siyasance a jihar.

Rikicin ya sanya yaran gwamna Fubara barin jam’iyar PDP, inda suka yi takara a jam’iyar APP.

Mai rahoto;

Salihu Garba. A

At-tajdid News.

You Might Also Like

NASSI Hails Governor Namadi’s Progressive Policies for Small Businesses

Ramadan Feeding: Jigawa Plans to Put 8 Million Meals on the Tables of the Need

RT Hon Dangyatin Emerged Chaiman Progressive Speakers Conference

Jigawa Appoints Emir Of Dutse As 2026 Amirul Hajji

UNICEF Urges Media to Advocate for Increased Water, Sanitation, and Hygiene Budget.

Attajdid October 8, 2024 October 8, 2024
Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Follow US

Find US on Social Medias
Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow

Weekly Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

Popular News
International News

Shugaba Paul Biya ya Koma Kamaru Bayan Shafe Makonni ba ya nan

Attajdid Attajdid October 22, 2024
Shugabannin Duniya Sun yi Allah Wadai da Harin Ta’addanci da Aka Kai Turkiyya
Takaitattun Abubuwan da Suka Faru a Khan Yunis Dake Gaza.
Gumel Emirate Foundation Honours Abacha”s Transport Minister, Gen. Gumel
Wani mutum mai shekara 50 ya yi yungurin Kashe kan sa
- Advertisement -
Ad imageAd image
Global Coronavirus Cases

Confirmed

0

Death

0

More Information:Covid-19 Statistics

Categories

  • U.K News
  • Today News
  • Hot News
  • Video

About US

Attajdid News, a Nigerian media outlet, is dedicated to fostering dialogue among diverse communities, promoting integrity, transparency, and critical thinking.

Subscribe US

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

© Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?