(kashi na farko)
Ta hanyar wani salon cin hanci da rashawa da yaudara, Isra’ila ta tsunduma cikin kasuwancin lu’u-lu’u mai araha a cikin DRC.
Ga yadda suke girbar ribar a bulusWasu masu hakar zinari suke tona wani rami a ma’adinan Chudja da ke yankin Kilomoto kusa da kauyen Kobu, mai tazarar kilomita 100 daga Bunia a arewa maso gabashin Kongo. Daga Zeynep ConkarIsra’ila na daga cikin kasashe biyar masu fitar da gogaggen lu’ulu’u duk da rashin albarkatun lu’u-lu’u nata na kanta.
Ta yaya hakan ke aiki?Wani rahoto na Kimberley Process (wani shiri na duniya na hana “lu’ulu’un jini” shiga kasuwa) ya bayyana cewa shida daga cikin manyan kasashe goma masu samar da lu’u-lu’u na Afirka ne, inda har yanzu yankuna da dama ke fama da rikici kan yankuna masu arzikin lu’u-lu’u.
A cikin shekarun da suka gabata, Isra’ila ta ƙara fadada kasancewarta a Afirka ta hanyar sabbin saka hannun jari kuma ta sami riba sosai daga ma’adinan lu’u-lu’u na Afirka.Kasuwancin da take yi don sayen kayan yaƙi na soji, ana zargin kamfanonin Isra’ila da ke da alaƙa da sojoji sun sami damar yin amfani da lu’u-lu’u da sauran ma’adanai a farashi mai muhimmanci, wanda ke taimaka wa masana’antar lu’u-lu’u ta Isra’ila bunƙasa.
A sakamakon haka, masana’antar lu’u-lu’u ta Isra’ila tana da hannu dumu-dumu a cinikin lu’u-lu’u na jini—kasuwancin da ke cike da wahalar ɗawainiyar miliyoyin mutane.An bullo da kalmar “lu’u lu’un jini” ne saboda nuna yadda ake amfani da kasuwancinsa wajen take hakkin bil’adama a duniya, musamman a kasashen Afirka da ke fama da yaƙe-yaƙe.
Batun lu’u-lu’u na jini da kuma hako ma’adanai masu daraja ba bisa ka’ida ba a yankunan da ake fama da rikici irin su Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango (DRC) ya kasance cikin rubuce-rubuce a cikin shekaru da dama, in ji Habibu Djuma, wani mai bincike a Cibiyar Koyarwa da Horar da Harkokin Kasuwanci ta Afirka (AKEM).
Waɗannan ma’adanai galibi ana hako su ne a cikin yanayi na tashin hankali, tare da amfani da ribar da ake samu don tallafa wa ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai da ke taimakawa wajen tsawaita rikici,” in ji Djuma.
DRC tana fama da kungiyoyi da dama masu dauke da makamai, musamman a yankunan gabashin kasar, musamman kungiyar M23, wadda ke da karfi a lardin Kivu ta Arewa, tare da wasu bangarori na lardin Ituri da Kudancin Kivu, a cewar Espoir Ngalukiye, wani mai fafutukar siyasa a DRC.“Wadannan kungiyoyi masu dauke da makamai sun yi ƙaurin suna wajen take hakkin dan adam da suke yi.
Suna da hannu cikin tashe-tashen hankula da suka hada da kashe fararen hula da cin zarafi ta hanyar jima’i, suna aikata laifukan cin zarafin bil’adama da dama,” in ji Ngalukiye.
Waɗannan lu’u-lu’u suna rura wutar yaƙin basasa kuma suna ba da gudunmawa ga yaɗuwar wahala, musamman a ƙasashe kamar Saliyo, Angola, da Jamhuriyar Dimokuradiyyar Cango.
“Lu’u lu’u da ke dabaibaye da rikice-rikice, wanda kuma aka fi sani da lu’ulu’u na jini, lu’ulu’u ne da ake haƙowa a wuraren da ake yaƙi ana sayar da su don samun kudin shiga ga masu tayar da kayar baya da shugabannin yaki, ko kuma sojojin mamaya.
Al’ummar duniya, ta hanyar tsarin tabbatar da tsarin Kimberley, sun dauki matakan daƙile kwararar wadannan lu’u-lu’u, amma duk da haka, haramtacciyar cinikayya ta ci gaba, musamman a yankunan da ake rikici kamar DRC,” in ji Djuma.
Djuma ya ambaci cewa, alal misali, Uganda da Ruwanda, a tarihi suna da hannu wajen fasa ƙwaurin ma’adanai daga DRC, kuma kasashen biyu suna da alaka ta diflomasiyya da tsaro da Isra’ila.”
A cikin wannan yanayin, tasirin Isra’ila ba lallai ba ne ya kasance a bayyane. Madadin haka, yana iya yin aiki ta hanyar masu zaman kansu, kasuwanci, ko hanyoyin sadarwar sirri waɗanda ke cin gajiyar rashin zaman lafiya a yankin, ”in ji Djuma.
TRT Afarka Hausa.
A biyomu zamu cigaba.
At-tajdid News.




