‘Ƙungiyar Houthi ta Yamen ta sanar da cewa ta harbo wani jirgin Amurka mara matuƙi da ke “kai hare-hare” a tsakiyar Yamen.
Mai magana da yawun dakarun Houthi Yahya Sarea ya ce tsaron Yemen na sama “ya samu nasarar” kakkaɓo jirgin Amurka mara matuƙi MQ-9 a sararin samaniyar Marib.
Sarea ya tabbatar da cewa dakarun Houthi sun ci gaba da sauke nauyinsu “na goyon bayan wahalar da Falasaɗinawa suke sha da kuma tsare Yamen.”A wani ɓangare na jaddada goyon baya ga Gaza, wanda ke fuskantar munanan hare-haren da Isra’ila ke kai wa tun daga 7 ga Oktoba, ‘yan Houthi sun ringa kai hare-hare da makamai masu linzami da jirage masara matuƙa kan jiragen ruwan Isra’ila ko waɗanda ke da alaƙa da Isra’ila da ke bi ta Bahrul Aswad, da Bahar Maliya da Tekun India,Tun daga farkon 2024, wani ƙawance da Amurka ke jagoranta ya ringa kai hare-hare ta sama suna da’awar kai wa wuraren da ‘yan Huti suke hare-hare a Yemen a matsayin martani ga hare-haren teku, waɗanda a wasu lokutan ‘yan Houthi suke mayar da martani.
Yaƙin Isra’ila a Gaza ya shiga rana ta 338, inda ta kashe kusan Falasɗinawa 41,000 yawaicinsu mata da yara tare da jikkata kusan 95,000, kuma wani ƙiyasi ya nuna cewa fiye da mutum 10,000 na ƙarƙashin ɓaraguzan gine-ginen da aka rusa.
An kai gawawwakin Falasɗinawan da suka mutu a harin Isra’ila, zuwa Asibitin Shahidai na al-Aqsa a Deir Balah, Gaza ranar 06 ga Satumba, 2024.
TRT Afrika Hausa.
At-tajdid News.




