Yarinyar mai shekaru 12 mai suna Bana Amjad Labum, an kashe ta da harsasan mamaya a lokacin da take cikin gidanta da ke garin Qaryut na gundumar Nablus.Sabbin hotuna sun nuna irin mumunar cin zarafin da ake yiwa fursunonin Falasdinu a cikin gidan yarin “Magiddo” na Isra’ila.
Jaridar Yedioth Ahronoth ta kawo yadda ‘Yan sandan mamaya sun kama mutane 110 a makon da ya gabata bayan da suka shiga zanga-zangar neman yarjejeniyar musayar fursunoni tare da turjiya.Majiyar manema labarai ta kawo wani jirgin sama mai saukar ungulu ya sauka a asibitin Shaare Zedek domin jigilar sojojin da suka jikkata.A bisa zalunci..
. ‘yan mamaya sun lalata gawar shahidi Majed Abu Zeina (mai shekaru 17) a sansanin Al-Faraa da ke kudu da Tubas a yammacin gabar kogin Jordan kwanakin baya.
Rundunar Jenin Battalion in the Jerusalem Brigades ta wallafa cewa: “Kuma ku shirya musu duk wani ƙarfi da za ku iya da kuma na dawakai, wanda za ku tsoratar da maƙiyan Allah da maƙiyanku da sauran waɗanda ba su ba, kun san su, Allah Ya san su.Ya Allah ka kasance tare da ‘yan uwanmu a Gaza, ka tabbatar da kafafunsu.”
Addu’ar da matasan kasar Jordan suka yi a lokacin wani gagarumin tsayuwar daka a gaban ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Amman, domin nuna goyon bayansu ga ‘yan adawa da kuma yin tir da harin da ‘yan mamaya ke kaiwa Gaza da yammacin kogin Jordan.
At-tajdid News.




