A yaƙin da Isra’ila ta kwashe kwana 332 tana yi a Gaza ta kashe Falasɗinawa fiye da 40,738 yawancinsu mata da yara sannan ta jikkata mutum fiye da 94,154, kuma ana da tabbacin mutum 10,000 na danne a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine da ta rusa.
Ma’aikatan ceto sun ci gaba da gudanar da aikin tono wasu mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine, yayin da Isra’ila ke barazanar ci gaba da kai hare-hare a yankin.
A ranar Litinin, 2 ga watan Satumba, 2024 dakarun Isra’ila sun kashe fararen-hula biyu tare da jikkata wasu bayan sun jefa bama-bamai a wani gida da ke arewa maso yammacin Birnin Gaza, a cewar kamfanin dillancin labarai na Falasɗinu WAFA.
Rundunar kare fararen-hula ta yankin ta ce ta ɗauko gawawwaki guda biyu da kuma mutanen da suka jikkata daga gidan iyalan Araj da ke Jalaa Street bayan Isra’ila ta kashe su.
Daga bisani adadin mutanen da suka mutu ya ƙaru zuwa 11 bayan jiragen yaƙin Isra’ila sun kai hari a Makarantar Safad da ke kudu maso gabashin Gaza, inda ‘yan gudun hijira suka sami mafaka.
Ma’aikatan ceto sun ci gaba da gudanar da aikin tono wasu mutanen da suka maƙale a ƙarƙashin ɓaraguzan gine-gine, yayin da Isra’ila ke barazanar ci gaba da kai hare-hare a yankin.Ministan harkokin wajen Saudiyya na yunƙurin ganin an daina kai hare-hare a Gaza.
Ministan harkokin wajen Saudiyya Yarima Faisal bin Farhan ya tattauna ta wayar tarho da takwarorinsa na Turkiyya, Masar, Jordan, Bahrain da Gambia ranar Lahadi a yunƙurin ganin Isra’ila ta daina kai hare-hare a Gaza da kuma bai wa Falasɗinawa ‘yanci.
Bin Farhan ya yi magana da Ministan Harkokin Wajen Turkiyya Hakan Fidan game da bayanai na baya-bayan nan halin da Falasɗinawa suke ciki, inda ya mayar da hankali kan yunƙurin ƙasashen Musulmai na ganin sun maido da martabar Falasɗinawa da kuma haɗa-kai don kawo ƙarshen hare-hare da keta hakkin da Isra’ila take yi wa Falasɗinawa.
Da yake tattaunawa da Ministan Harkokin Wajen Masar Badr Abdelatty, ya mayar da hankali kan halin da yankunan Falasɗinawa suke ciki da kuma buƙatar ɗaukar matakan gaggawa domin dakatar da rashin mutuncin da Isra’ila take yi wa Falasɗinawa, yayin da kuma ya jaddada buƙatar samar da ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kanta.
Kazalika a yayin da yake magana da Ministan Harkokin Wajen Jordan Ayman Safadi ya bayyana buƙatar gagauta tsagaita wuta da kuma haɗin-kan dukkan ƙasashen Larabawa da na Musulmai wajen ganin an yi wa Falasɗinawa adalci, ciki har da ƙirƙiro musu ƙasa mai cin gashin kanta.
A cewar majiyarmu daga ‘yankin gabas ta tsakiya.
At-tajdid News.




