A wani samame na hadin gwiwa da bangarorin gwagwarmayar Falasdinawan suka kai a Gaza, inda suka kashe tare da jikkata sojojin yahudawan sahyoniya 6 ya zuwa lokacin da ake hada rahotan.Daga bangaran Mujahidan Al-Qassam sun yi nasarar kashe wasu sojojin yahudawan sahyoniya biyu da suka makale a wani gini da ke bayan dakin taro na Stars da ke kudancin unguwar Zaytoun a birnin Gaza.
Al-Quds Brigades,sun tayar da wani babban bam wanda aka dasa tare da motar sojojin mamaya ta kutsa kai cikin titin Al-Sikka (yankin Triangle) a unguwar Al-Zaytoun, gabashin birnin Gaza inda aka sami wadanda suka mutu da kuma jikkata alamarin da yasa an bukaci jami’an ceto.
Za a bayyana sunayen sojojin haya 163 da aka kashe a Gaza sun fito ne daga kasashe daban-daban, akasarinsu daga kasashen Turai, domin halartar kisan gillar da ake yiwa Falasdinawan da ba su da kariya a Gaza domin neman kudi.
Kungiyar gwagwarmayar Palastinu ta fitar da sanarwar gargadin masu adawa da ita a duk fadin yammacin kogin Jordan da kuma gargadin ‘yan uwa masu gwagwarmaya a yammacin kogin Jordan da kada su yi amfani da wayoyi da hanyoyin sadarwa iri-iri masu saukin ganowa ta hanyar leken asirin sojojin Isra’ila don haka su yi amfani ta hanyar resistors su kai musu hari.
Ma’aikatar Lafiya ta Falasdinu a Yammacin Gabar Kogin Jordan ta bayyana dakarun mamaya sun toshe hanyoyin zuwa asibitin Ibn Sina da ke Jenin tare da yiwa asibitin Khalil Suleiman kawanya.
Ma’aikatar kara da cewa an sami Shahidai 58 a Gaza da jikkata 131 suka isa asibitoci a kisan kiyashin Sahayoniya na karun mutane 4 a cikin sa’o’i 24 da suka gabata.
Adadin wadanda Yahudawan sahyoniyya suka kashe a Gaza ya karu zuwa shahidai 40,534 sannan wasu 93,778 suka samu raunuka tun bayan da aka fara yakin kisan kare dangi a ranar 7 ga Oktoba zuwa yau.
At-tajdid News.




